ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kifi Na Ganin Ka Mai Jar Koma!

by Sulaiman and CGTN Hausa
9 months ago
Kifi

Tarihi ba ya gushewa saboda kawai wasu sun kawar da kai daga gare shi. Kalaman baya bayan nan da ake ji daga wasu jagororin Japan, dangane da batun yankin Taiwan na kasar Sin abun damuwa ne. Kuma sun baiwa duniya mamaki kwarai da gaske, ganin cewa Japan a matsayinta na kasa wadda ta sha kaye a karshen yakin duniya na biyu, a yanzu wai ita ce ke kokarin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin. Abun lurar a nan shi ne a tarihi kafin Japan ta mamaye Taiwan, babu wata matsala tsakanin Sin da Japan, amma bayan mamayar, Japan ta kafa mummunan tarihin muzgunawa, da cutar da bil’adama, tare da haifar da rarrabuwar kawuna a shiyyar da take.

A cikin shekarar 1895 ne Japan ta kwace yankin Taiwan daga gwamnatin daular Qing ta lokacin, karkashin wata yarjejeniyar rashin adalci ta Shimonoseki. Bayan mamayar Japan, yankin na Taiwan ya fada matsanancin hali da tashe-tashen hankula, da kwashe albarkatun kasa, da kokarin kawar da al’adun al’ummun yankin. Don haka, wani bangare da tarihin Taiwan ba zai manta da shi ba, shi ne mugun raunin da Japan ta yiwa yankin Taiwan, da rashin adalcin da ta bari a tarihinsa.

A yayin yakin duniya na biyu, sama da al’ummun Taiwan 300,000 Japan ta tursasawa shiga ayyukan soji, kuma kusan 30,000 daga cikinsu sun rasu a kasashen ketare. Baya ga dubban matan Taiwan da dakarun Japan din suka tursasawa zama bayi da ake cin zarafinsu.

ADVERTISEMENT

Dukkanin wadannan, ta’asa ce da tarihi ya kiyaye, wadanda har abada al’ummun duniya ba za su taba mantawa da su ba. Bayan da Japan ta mika wuy;a a karshen yakin duniya na biyu cikin shekarar 1945, bayan shafe shekaru 50 tana mulkin mallaka ga Taiwan, al’ummun yankin na Taiwan sun cika da murna da san barka. Wanda hakan ya zama shaidar kubutarsu daga mulkin danniya, da komawa cikin ’yan uwa dake sauran yankunan kasar Sin.

Bisa wadannan abubuwa da suka faru a tarihi, za mu gane cewa, duk yadda aka yi kokarin yiwa tarihi gyaran fuska, ba za a iya maye gurbin gaskiya da karya ba, kana ba za a iya binne adalci ba. Tarin laifukan da Japanawa ’yan mamaya suka aikata ga al’ummun Taiwan ba zai bace ba, ko a sauya shi ta hanyar amfani da wasu kalamai na farfaganda.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Abun da zai iya sassauta radadin ta’asar Japan shi ne yin karatun baya, da tuba na hakika, da gyara kura-kurai. Kazalika, ya zama wajibi Japan ta fuskanci gaskiyar tarihi, ta yi tunani, da kokarin biyan bashin tarihi, ta yadda za a kai ga warware dukkanin batutuwa masu nasaba da hakan. (Saminu Alhassan)

Kifi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy
Kifi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Farfesa Ibrahim Tsafe A Matsayin Sabon Shugaban Jami’ar ZAMSUT

Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Farfesa Ibrahim Tsafe A Matsayin Sabon Shugaban Jami’ar ZAMSUT

LABARAI MASU NASABA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.