Gidauniyar Sheikh Dahiru Usman Bauchi za ta gudanar da taronta na Zikirin Juma’a na shekara a fadar Sarki Alhaji Aminu Ado Bayero da ke Nasarawa. An shirya gudanar da taron ne a gobe Juma’a, 5 ga Yuli, 2024, da karfe 4:00 na yamma.
Taron dai zai kasance ƙarƙashin jagorancin Babban Jagoran Tijjaniyya a Najeriya Sheikh Dahiru Usman Bauchi wanda zai kasance babban baƙo na musamman. Manyan baƙin da zasu halarci taron sun haɗa da; Alhaji Aminu Ado Bayero, da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.
- Tinubu Ya Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Babban Ɗan Jarida Kabir Yusuf
- NAFDAC Ta Yi Bikin Lalata Kayayyakin Jabu Na ₦985.3m A Kano
Taron Zikirin zai mayar da hankali ne kan karatuttuka da addu’o’i da nufin magance matsalolin tsaron da Nijeriya ke fuskanta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp