• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Kaddamar Da Kwamitin Gyaran Mafi Karancin Albashi Ranar Talata

by Muhammad
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Tinubu Zai Kaddamar Da Kwamitin Gyaran Mafi Karancin Albashi Ranar Talata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijeriya za ta kaddamar da wani kwamiti mai wakilai 37 da zai aiki kan mafi karancin albashin ma’aikata na kasa da bayar da shawarwari kan karin mafi karancin albashi a Nijeriya.

Wata sanarwa da daraktan yada labarai na ofishin sakataren gwamnatin tarayya, Segun Imohiosen, ya fitar, ya bayyana cewa kaddamar da kwamitin na cikin umarnin da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar na kafa shi.

  • Karin Albashi: Ma’aikatan Nijeriya Za Su Dara a 2024 – Tinubu
  • Tinubu Ya Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya Bisa Kin Katsalandan A Shari’ar Gwamnoni – Kabiru Marafa

Ranar Talata aka shirya bikin kaddamar da kwamitin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

A cewar sanarwar, Bukar Goni Aji, tsohon shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ne zai shugabanci kwamitin da mambobinsa daga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihohi da kamfanoni masu zaman kansu da kungiyoyin kwadago.

Sanarwar ta ce, “Daga bangaren Gwamnatin Tarayya, mambobin sun hada da Nkeiruka Onyejeocha da Karamin Ministan Kwadago da Aiki, Hon. Wale Edun da Ministan Kudi.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Sauran ‘yan kwamitin sun hada da “Ministan Tsare-tsaren da Kasafin Kudi Atiku Bagudu da shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya Yemi Esan da kuma Babban Sakatare, GSO. OSGF, Nnamdi Maurice Mbaeri da Ekpo Nta, shugaban NSIWC a matsayin Sakatariya.

“Haka kuma daga bangaren gwamnatin jiha, gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ne zai wakilici gwamnonin Arewa ta tsakiya sai gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, a matsayin wakilin jihohin Arewa maso Gabas da Alh. Umar Dikko Radda, Gwamnan Jihar Katsina, a matsayin wakilin Arewa maso Yamma, sauran sun hada da Charles Soludo, gwamnan jihar Anambra, a matsayin wakilin yankin Kudu maso Gabas, sai kuma Sanata Ademola Adeleke, Gwamnan jihar Osun a matsayin wakilin yankin Kudu maso Yamma, sai gwamna jihar Cross River, Otu Bassey Edet a matsayin wakili daga Kudu maso Yamma.

“Daga kungiyar tuntubar ma’aikata ta Nijeriya (NECA) – Adewale-Smatt Oyerinde, Darakta-Janar na NECA da Chuma Nwankwo da Thompson Akpabio tare da mambobi daga Kungiyar ‘yan Kasuwa, Masana’antu, Ma’adinai da Noma ta Nijeriya (NACCIMA) wadanda suka hada da Shugaban kasa, Asiwaju (Dr) Michael Olawale-Cole da Hon. (Dr) Ahmed Rabiu, Mataimakin Shugaba kuma Babban jami’a a Humphrey Ngonadi (NPOM).”

Sanarwar ta kara da cewa mambobin kwamitin sun hada da kungiyar masu kananan sana’o’i ta kasa (NASME) su ne Abdulrashid Yerima, Shugaban Majalisar, sai Theophilus Nnorom Okwuchukwu, wakilin kamfanoni masu zaman kansu; Dr. Muhammed Nura Bello, a matsayin mataimakin shugaban daga shiyyar arewa maso yamma.

Kazalika, daga kungiyar masu ‘yan kasuwa ta Nijeriya (MAN) akwai Misis Grace Omo-Lamai, Daraktar Ma’aikata ta Kamfanin Breweries ta Nijeriya; Segun Ajayi-Kadir da Darakta-Janar, MAN; Lady Ada Chukwudozie da Manajan Darakta, Dozzy, a bangaren Oyal da iskar gas.

“Daga kungiyar kwadago, kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) Kwamared Joe Ajaero, shugaban kungiyar NLC da Kwamared Emmanuel Ugboaja da Kwamared Prince Adeyanju Adewale da Kwamared Ambali Akeem Olatunji da Kwamared Benjamin Anthony da Farfesa Theophilius Ndukuba.

“Kazalika, mambobin kwamitin daga kungiyar ‘yan kasuwa ta Nijeriya (TUC) sun hada da shugaban kungiyar TUC, Kwamared (Engr) Festus Osifo da Mataimakin Shugaban TUC, Kwamared Tommy Etim Okon da Kwamared Kayode Surajudeen Alakija, mataimakin kungiyar ta kasa .na II da Kwamared Jimoh Oyibo, mataimakin shugaban kasa na III, sai Kwamared Nuhu A. Toro, Sakatare Janar da Kwamared Hafusatu Shuaib, shugabar mata ta Women Comm,” cewar sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KwamitiMafi Karancin AlbashiNijeriyaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Kaddamar Da Biki Kafin Liyafar Bikin Bazara A New York

Next Post

AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

7 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

20 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

21 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Next Post
AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.