• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Kaddamar Da Kwamitin Gyaran Mafi Karancin Albashi Ranar Talata

by Muhammad
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Tinubu Zai Kaddamar Da Kwamitin Gyaran Mafi Karancin Albashi Ranar Talata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijeriya za ta kaddamar da wani kwamiti mai wakilai 37 da zai aiki kan mafi karancin albashin ma’aikata na kasa da bayar da shawarwari kan karin mafi karancin albashi a Nijeriya.

Wata sanarwa da daraktan yada labarai na ofishin sakataren gwamnatin tarayya, Segun Imohiosen, ya fitar, ya bayyana cewa kaddamar da kwamitin na cikin umarnin da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar na kafa shi.

  • Karin Albashi: Ma’aikatan Nijeriya Za Su Dara a 2024 – Tinubu
  • Tinubu Ya Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya Bisa Kin Katsalandan A Shari’ar Gwamnoni – Kabiru Marafa

Ranar Talata aka shirya bikin kaddamar da kwamitin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

A cewar sanarwar, Bukar Goni Aji, tsohon shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ne zai shugabanci kwamitin da mambobinsa daga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihohi da kamfanoni masu zaman kansu da kungiyoyin kwadago.

Sanarwar ta ce, “Daga bangaren Gwamnatin Tarayya, mambobin sun hada da Nkeiruka Onyejeocha da Karamin Ministan Kwadago da Aiki, Hon. Wale Edun da Ministan Kudi.

Labarai Masu Nasaba

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

Sauran ‘yan kwamitin sun hada da “Ministan Tsare-tsaren da Kasafin Kudi Atiku Bagudu da shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya Yemi Esan da kuma Babban Sakatare, GSO. OSGF, Nnamdi Maurice Mbaeri da Ekpo Nta, shugaban NSIWC a matsayin Sakatariya.

“Haka kuma daga bangaren gwamnatin jiha, gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ne zai wakilici gwamnonin Arewa ta tsakiya sai gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, a matsayin wakilin jihohin Arewa maso Gabas da Alh. Umar Dikko Radda, Gwamnan Jihar Katsina, a matsayin wakilin Arewa maso Yamma, sauran sun hada da Charles Soludo, gwamnan jihar Anambra, a matsayin wakilin yankin Kudu maso Gabas, sai kuma Sanata Ademola Adeleke, Gwamnan jihar Osun a matsayin wakilin yankin Kudu maso Yamma, sai gwamna jihar Cross River, Otu Bassey Edet a matsayin wakili daga Kudu maso Yamma.

“Daga kungiyar tuntubar ma’aikata ta Nijeriya (NECA) – Adewale-Smatt Oyerinde, Darakta-Janar na NECA da Chuma Nwankwo da Thompson Akpabio tare da mambobi daga Kungiyar ‘yan Kasuwa, Masana’antu, Ma’adinai da Noma ta Nijeriya (NACCIMA) wadanda suka hada da Shugaban kasa, Asiwaju (Dr) Michael Olawale-Cole da Hon. (Dr) Ahmed Rabiu, Mataimakin Shugaba kuma Babban jami’a a Humphrey Ngonadi (NPOM).”

Sanarwar ta kara da cewa mambobin kwamitin sun hada da kungiyar masu kananan sana’o’i ta kasa (NASME) su ne Abdulrashid Yerima, Shugaban Majalisar, sai Theophilus Nnorom Okwuchukwu, wakilin kamfanoni masu zaman kansu; Dr. Muhammed Nura Bello, a matsayin mataimakin shugaban daga shiyyar arewa maso yamma.

Kazalika, daga kungiyar masu ‘yan kasuwa ta Nijeriya (MAN) akwai Misis Grace Omo-Lamai, Daraktar Ma’aikata ta Kamfanin Breweries ta Nijeriya; Segun Ajayi-Kadir da Darakta-Janar, MAN; Lady Ada Chukwudozie da Manajan Darakta, Dozzy, a bangaren Oyal da iskar gas.

“Daga kungiyar kwadago, kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) Kwamared Joe Ajaero, shugaban kungiyar NLC da Kwamared Emmanuel Ugboaja da Kwamared Prince Adeyanju Adewale da Kwamared Ambali Akeem Olatunji da Kwamared Benjamin Anthony da Farfesa Theophilius Ndukuba.

“Kazalika, mambobin kwamitin daga kungiyar ‘yan kasuwa ta Nijeriya (TUC) sun hada da shugaban kungiyar TUC, Kwamared (Engr) Festus Osifo da Mataimakin Shugaban TUC, Kwamared Tommy Etim Okon da Kwamared Kayode Surajudeen Alakija, mataimakin kungiyar ta kasa .na II da Kwamared Jimoh Oyibo, mataimakin shugaban kasa na III, sai Kwamared Nuhu A. Toro, Sakatare Janar da Kwamared Hafusatu Shuaib, shugabar mata ta Women Comm,” cewar sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KwamitiMafi Karancin AlbashiNijeriyaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Kaddamar Da Biki Kafin Liyafar Bikin Bazara A New York

Next Post

AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

Related

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

32 seconds ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

2 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

16 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

19 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

23 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

1 day ago
Next Post
AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.