• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Kaddamar Da Kwamitin Gyaran Mafi Karancin Albashi Ranar Talata

by Muhammad
2 years ago
Tinubu

Gwamnatin Nijeriya za ta kaddamar da wani kwamiti mai wakilai 37 da zai aiki kan mafi karancin albashin ma’aikata na kasa da bayar da shawarwari kan karin mafi karancin albashi a Nijeriya.

Wata sanarwa da daraktan yada labarai na ofishin sakataren gwamnatin tarayya, Segun Imohiosen, ya fitar, ya bayyana cewa kaddamar da kwamitin na cikin umarnin da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar na kafa shi.

  • Karin Albashi: Ma’aikatan Nijeriya Za Su Dara a 2024 – Tinubu
  • Tinubu Ya Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya Bisa Kin Katsalandan A Shari’ar Gwamnoni – Kabiru Marafa

Ranar Talata aka shirya bikin kaddamar da kwamitin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

A cewar sanarwar, Bukar Goni Aji, tsohon shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ne zai shugabanci kwamitin da mambobinsa daga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihohi da kamfanoni masu zaman kansu da kungiyoyin kwadago.

Sanarwar ta ce, “Daga bangaren Gwamnatin Tarayya, mambobin sun hada da Nkeiruka Onyejeocha da Karamin Ministan Kwadago da Aiki, Hon. Wale Edun da Ministan Kudi.

LABARAI MASU NASABA

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

Sauran ‘yan kwamitin sun hada da “Ministan Tsare-tsaren da Kasafin Kudi Atiku Bagudu da shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya Yemi Esan da kuma Babban Sakatare, GSO. OSGF, Nnamdi Maurice Mbaeri da Ekpo Nta, shugaban NSIWC a matsayin Sakatariya.

“Haka kuma daga bangaren gwamnatin jiha, gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ne zai wakilici gwamnonin Arewa ta tsakiya sai gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, a matsayin wakilin jihohin Arewa maso Gabas da Alh. Umar Dikko Radda, Gwamnan Jihar Katsina, a matsayin wakilin Arewa maso Yamma, sauran sun hada da Charles Soludo, gwamnan jihar Anambra, a matsayin wakilin yankin Kudu maso Gabas, sai kuma Sanata Ademola Adeleke, Gwamnan jihar Osun a matsayin wakilin yankin Kudu maso Yamma, sai gwamna jihar Cross River, Otu Bassey Edet a matsayin wakili daga Kudu maso Yamma.

“Daga kungiyar tuntubar ma’aikata ta Nijeriya (NECA) – Adewale-Smatt Oyerinde, Darakta-Janar na NECA da Chuma Nwankwo da Thompson Akpabio tare da mambobi daga Kungiyar ‘yan Kasuwa, Masana’antu, Ma’adinai da Noma ta Nijeriya (NACCIMA) wadanda suka hada da Shugaban kasa, Asiwaju (Dr) Michael Olawale-Cole da Hon. (Dr) Ahmed Rabiu, Mataimakin Shugaba kuma Babban jami’a a Humphrey Ngonadi (NPOM).”

Sanarwar ta kara da cewa mambobin kwamitin sun hada da kungiyar masu kananan sana’o’i ta kasa (NASME) su ne Abdulrashid Yerima, Shugaban Majalisar, sai Theophilus Nnorom Okwuchukwu, wakilin kamfanoni masu zaman kansu; Dr. Muhammed Nura Bello, a matsayin mataimakin shugaban daga shiyyar arewa maso yamma.

Kazalika, daga kungiyar masu ‘yan kasuwa ta Nijeriya (MAN) akwai Misis Grace Omo-Lamai, Daraktar Ma’aikata ta Kamfanin Breweries ta Nijeriya; Segun Ajayi-Kadir da Darakta-Janar, MAN; Lady Ada Chukwudozie da Manajan Darakta, Dozzy, a bangaren Oyal da iskar gas.

“Daga kungiyar kwadago, kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) Kwamared Joe Ajaero, shugaban kungiyar NLC da Kwamared Emmanuel Ugboaja da Kwamared Prince Adeyanju Adewale da Kwamared Ambali Akeem Olatunji da Kwamared Benjamin Anthony da Farfesa Theophilius Ndukuba.

“Kazalika, mambobin kwamitin daga kungiyar ‘yan kasuwa ta Nijeriya (TUC) sun hada da shugaban kungiyar TUC, Kwamared (Engr) Festus Osifo da Mataimakin Shugaban TUC, Kwamared Tommy Etim Okon da Kwamared Kayode Surajudeen Alakija, mataimakin kungiyar ta kasa .na II da Kwamared Jimoh Oyibo, mataimakin shugaban kasa na III, sai Kwamared Nuhu A. Toro, Sakatare Janar da Kwamared Hafusatu Shuaib, shugabar mata ta Women Comm,” cewar sanarwar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
Manyan Labarai

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
Manyan Labarai

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Next Post
AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

LABARAI MASU NASABA

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.