ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Kaddamar Da Kwamitin Gyaran Mafi Karancin Albashi Ranar Talata

by Muhammad
2 years ago
Tinubu

Gwamnatin Nijeriya za ta kaddamar da wani kwamiti mai wakilai 37 da zai aiki kan mafi karancin albashin ma’aikata na kasa da bayar da shawarwari kan karin mafi karancin albashi a Nijeriya.

Wata sanarwa da daraktan yada labarai na ofishin sakataren gwamnatin tarayya, Segun Imohiosen, ya fitar, ya bayyana cewa kaddamar da kwamitin na cikin umarnin da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar na kafa shi.

  • Karin Albashi: Ma’aikatan Nijeriya Za Su Dara a 2024 – Tinubu
  • Tinubu Ya Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya Bisa Kin Katsalandan A Shari’ar Gwamnoni – Kabiru Marafa

Ranar Talata aka shirya bikin kaddamar da kwamitin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, Bukar Goni Aji, tsohon shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ne zai shugabanci kwamitin da mambobinsa daga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihohi da kamfanoni masu zaman kansu da kungiyoyin kwadago.

Sanarwar ta ce, “Daga bangaren Gwamnatin Tarayya, mambobin sun hada da Nkeiruka Onyejeocha da Karamin Ministan Kwadago da Aiki, Hon. Wale Edun da Ministan Kudi.

LABARAI MASU NASABA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Sauran ‘yan kwamitin sun hada da “Ministan Tsare-tsaren da Kasafin Kudi Atiku Bagudu da shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya Yemi Esan da kuma Babban Sakatare, GSO. OSGF, Nnamdi Maurice Mbaeri da Ekpo Nta, shugaban NSIWC a matsayin Sakatariya.

“Haka kuma daga bangaren gwamnatin jiha, gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ne zai wakilici gwamnonin Arewa ta tsakiya sai gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, a matsayin wakilin jihohin Arewa maso Gabas da Alh. Umar Dikko Radda, Gwamnan Jihar Katsina, a matsayin wakilin Arewa maso Yamma, sauran sun hada da Charles Soludo, gwamnan jihar Anambra, a matsayin wakilin yankin Kudu maso Gabas, sai kuma Sanata Ademola Adeleke, Gwamnan jihar Osun a matsayin wakilin yankin Kudu maso Yamma, sai gwamna jihar Cross River, Otu Bassey Edet a matsayin wakili daga Kudu maso Yamma.

“Daga kungiyar tuntubar ma’aikata ta Nijeriya (NECA) – Adewale-Smatt Oyerinde, Darakta-Janar na NECA da Chuma Nwankwo da Thompson Akpabio tare da mambobi daga Kungiyar ‘yan Kasuwa, Masana’antu, Ma’adinai da Noma ta Nijeriya (NACCIMA) wadanda suka hada da Shugaban kasa, Asiwaju (Dr) Michael Olawale-Cole da Hon. (Dr) Ahmed Rabiu, Mataimakin Shugaba kuma Babban jami’a a Humphrey Ngonadi (NPOM).”

Sanarwar ta kara da cewa mambobin kwamitin sun hada da kungiyar masu kananan sana’o’i ta kasa (NASME) su ne Abdulrashid Yerima, Shugaban Majalisar, sai Theophilus Nnorom Okwuchukwu, wakilin kamfanoni masu zaman kansu; Dr. Muhammed Nura Bello, a matsayin mataimakin shugaban daga shiyyar arewa maso yamma.

Kazalika, daga kungiyar masu ‘yan kasuwa ta Nijeriya (MAN) akwai Misis Grace Omo-Lamai, Daraktar Ma’aikata ta Kamfanin Breweries ta Nijeriya; Segun Ajayi-Kadir da Darakta-Janar, MAN; Lady Ada Chukwudozie da Manajan Darakta, Dozzy, a bangaren Oyal da iskar gas.

“Daga kungiyar kwadago, kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) Kwamared Joe Ajaero, shugaban kungiyar NLC da Kwamared Emmanuel Ugboaja da Kwamared Prince Adeyanju Adewale da Kwamared Ambali Akeem Olatunji da Kwamared Benjamin Anthony da Farfesa Theophilius Ndukuba.

“Kazalika, mambobin kwamitin daga kungiyar ‘yan kasuwa ta Nijeriya (TUC) sun hada da shugaban kungiyar TUC, Kwamared (Engr) Festus Osifo da Mataimakin Shugaban TUC, Kwamared Tommy Etim Okon da Kwamared Kayode Surajudeen Alakija, mataimakin kungiyar ta kasa .na II da Kwamared Jimoh Oyibo, mataimakin shugaban kasa na III, sai Kwamared Nuhu A. Toro, Sakatare Janar da Kwamared Hafusatu Shuaib, shugabar mata ta Women Comm,” cewar sanarwar.

Tinubu
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji
Manyan Labarai

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Next Post
AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

AFCON 2023: Guinea Ta Doke Equatorial Guinea A Wasan Zagaye Na 16

LABARAI MASU NASABA

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.