• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Ya Yi Barazanar Ƙarin Haraji Ga Ƙasashen Da Suka Rungumi BRICS

by Abubakar Sulaiman
4 months ago
Trump

Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar sanya ƙarin haraji na kashi 10% kan kowace ƙasa da ta goyi bayan manufofin ƙungiyar BRICS da ke adawa da muradun Amurka. Trump ya bayyana hakan ne ta shafinsa na sada zumunta, yana mai cewa ba za a samu wani rangwame ba ga kowace ƙasa da ke bin wannan hanya.

Ƙungiyar BRICS, wacce da farko ta ƙunshi ƙasashen Brazil, Rasha, Indiya, China da Afirka ta Kudu, yanzu ta karɓi ƙarin ƙasashe kamar Masar, Habasha, Indonesia, Iran, Saudiyya da haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE). Ƙungiyar na wakiltar fiye da rabin yawan al’ummar duniya kuma tana gudanar da taronta a birnin Rio de Janeiro, inda shugabannin ke kiran a sake fasalin manyan cibiyoyin ƙasa da ƙasa da kuma ƙin amincewa da haraji da ke haddasa taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

  • Tsarin BRICS Ya Zama Muhimmin Dandalin Hadin Kai Na Kasashe Masu Tasowa
  • Tsakanin Nijeriya Da BRICS+: Idan Zamani Ya Dinka Riga…

Wannan barazana daga Trump ta zo ne bayan BRICS ta soki manufofin harajin Amurka da kuma ƙoƙarinta na samar da tsarin kuɗin da zai maye gurbin Dalar Amurka. A cewarsa, irin wannan haɗin gwuiwa barazana ce ga Amurka kuma za ta fuskanci martani mai tsauri.

Masana sun bayyana cewa cire alaƙa da China, wacce ke ɗaya daga cikin manyan mambobin BRICS, ba abu ne mai sauƙi ba saboda tasirinta a fannonin fasahar zamani kamar motoci masu amfani da lantarki, da batir, da albarkatun ƙasa kamar sinadarai masu ɗauke da maganadisu.

Andrew Wilson daga Cibiyar Kasuwanci ta Duniya ya ce: “A aikace, sauya China a waɗannan fannonin yana da matuƙar wahala.” Duk da haka, Trump ya sha alwashin ɗaukar matakan tattalin arziƙi domin kare matsayin Amurka a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL
Manyan Labarai

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
Next Post
Sojoji Sun Fatattaki Ƴan Bindigar Da Suka Zo Sace Wani Ɗan China

Sojoji Sun Fatattaki Ƴan Bindigar Da Suka Zo Sace Wani Ɗan China

LABARAI MASU NASABA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.