ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Nijeriya Da BRICS+: Idan Zamani Ya Dinka Riga…

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
BRICS

”Idan zamani ya dinka riga, ya kamata a saka.” Wannan magana ta nuna hikimar Hausawa ta kokarin tafiya tare da zamani a ko yaushe. Sa’an nan yadda kasar Najeriya ta shiga tsarin BRICS+ a matsayin abokiyar hulda a kwanan nan, shi ma ya nuna hikimar tafiya tare da yanayin zamani sosai.

Ko mene ne yanayin zamani da Najeriya ta tafi da shi? Shi ne haskakawar tauraron kasashe masu tasowa, ko kuma “Global South” a bakin Turawa, a duniya.

  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu
  • Ba Ma Cikin Waɗanda Suka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga – Gwamnatin Katsina

Mun san rikicin hada-hadar kudi da ya abku a shekarar 2008 ya sa dimbin kasashe masu sukuni fuskantar matsalar koma bayan tattalin arzikinsu. Tun daga lokacin, wasu kasashen da tattalin arzikinsu ke tasowa cikin sauri, ciki har da kasar Sin, sannu a hankali suka fara zama wadanda ke samar da mafi yawan karuwar tattalin arzikin duniya. Daga bisani, wadannan kasashe sun yi amfani da tsarin hadin gwiwa na BRICS wajen wanzar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a duniya, da taimakon sauran kasashe masu tasowa wajen zamanantarwa, ta hanyar hadin gwiwa a fannonin cinikayya da masana’antu. A lokacin da ake aiwatar da wannan mataki, kasashe masu tasowa sun fara taka muhimmiyar rawa a fannin kulawa da al’amuran duniya, inda suke kokarin yin garambawul da zai tabbatar da adalci, da daidaituwa, gami da wakiltar mafi yawan kasashe.

ADVERTISEMENT

Yanzu kasar Najeriya ita ma ta shiga tsarin BRICS+, kuma hakan zai kara karfin tsarin hadin gwiwa na BRICS+, ganin yadda yawan al’ummarsa zai kai kaso 54.6% na daukacin al’ummar duniya, kana GDPnsa zai kai kaso 42.2% na adadin na duniya. Hakan zai sa kasashen BRICS da abokan huldarsu samun damar karfafa wa kasashe masu tasowa ikon fada-a-ji, da inganta wakilcinsu a hukumomin duniya, gami da sanya tsarin hada-hadar kudi na duniya ya dace da yanayin ci gaban kasashen da tattalin arzikinsu ke kan hanyar tasowa.

Sa’an nan a nata bangaren, Najeriya za ta samu alfanu a fannoni daban daban, ta hanyar zama abokiyar huldar kasashen BRICS, wadanda a kalla suka kunshi wadannan bangarori: Wato na farko, bisa tsarin gudanar da ciniki da kudin kashin kai na ko wace kasa da kasashen BRICS ke kokarin yayatawa, Najeriya za ta iya aiwatar da karin cinikin waje da kudinta na Naira, don rage dogaro kan dalar Amurka. Ta haka, kasar za ta samu damar sasanta matsalar karancin kudin musaya, wadda kan haddasa matsalar tafiyar hawainiya ga ci gaban tattalin arziki a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Na biyu, nan gaba Najeriya tana da damar samun bashi daga bankin raya kasa na NDB, da tsarin samar da kudi cikin gaggawa na CRA, duk a karkashin tsarin BRICS, don tallafa wa ayyukanta na gina kayayyakin more rayuwa, da dai sauransu.

Na uku, a matsayinta na babbar kasa mai dimbin al’umma da karfin tattalin arizki ta nahiyar Afirka, Najeriya na neman zama mai fada-a-ji a Majalisar Dinkin Duniya da sauran hukumomi na duniya. To, kasar tana da damar cika burinta a wannan fanni, bisa goyon bayan da za ta iya samu daga tsarin BRICS+.

Na hudu, idan an yi nazari tare da hangen nesa, to, za a ga yadda wasu abubuwan da tsarin BRICS+ ya kunsa, irinsu kasancewar mabambantan al’adu tare cikin daidaito, da cudanya tsakaninsu don neman koyi da juna, za su taimaki Najeriya, a kokarinta na lalubo hanyar raya kai, wadda za ta dace da ainihin yanayin da kasar ke ciki. Wannan shi ne dalilin da ya sa ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta furta cewa, zama abokiyar huldar kasashen BRICS “wani gwaji ne mafi kyau a kokarin kasar na tabbatar da tsare-tsaren raya kasa na kashin kanta”. (Bello Wang)

BRICS
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
BRICS
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Fashewar Tankar Mai A Suleja: An Kai Mutum 20 Manyan Asibitocin Abuja Don Samun Kulawa Ta Musamman

Fashewar Tankar Mai A Suleja: An Kai Mutum 20 Manyan Asibitocin Abuja Don Samun Kulawa Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.