• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Fetur Da Abinci: Gaskiya Muna Jin Jiki, In Ji ‘Yan Nijeriya

•Tsadar Kayan Masarufi Ta Karu Zuwa Kashi 22.7 Cikin 100

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Tsadar Fetur
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan Nijeriya sun shiga halin taraddudi a wannan makon yayin da farashin man fetur da kayayyakin masarufi suka yi tashin gwauron zabi.

Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta bayyana cewa hauhawan farashin kayan abinci a watan Yunin 2023, ya kai kashi 22.79 a cikin dari idan aka kwatanta da na watan Mayun 2023, da ya kasance da kashi 22.41 a cikin dari.
Wannan na kunshe a cikin rahoton farashin kayan abinci (CPI) na wata-wata da NBS ta fitar a makon nan. A cewar rahoton NBS, karin farashin ya kai kashi 0.38 a cikin dari, inda rahoton ya yi karin hasken cewa idan aka duba mizanin shekara-shekara, za a ga cewa farashin ya karu ne da kashi 4.19 a cikin dari, idan aka kwatanta da wanda aka samu a watan Yunin 2022 da bai wuce kashi 18.60 a cikin dari.
NBS ta ce, an samu karuwar farashin ne a kan kayayyaki kamar su, man girki, burodi, hatsi, dankali, doya, kifi, nama, kwai, kayan lambu da sauransu.

  • Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Kai Kashi 21.82 – NBS

Sauran harkokin da aka samu karin farashin su ne, sufuri, iskar gas, kayan gyaran ababen hawa, kiwon lafiya da bakin mai.
Sai dai ‘Yan Nijeriya ba su gama jimamin tsadar farashin kayan masarufin ba, kwatsam sai ga sanarwar karin farashin litar man fetur daga Naira 539 zuwa naira 617 a Babban Birnin Tarayya Abuja.
Ana kyautata zaton karin farashin man ba zai rasa nasaba da batun da ‘yan kasuwar man suka yi cewa farashin na iya kaiwa Naira 700 kan kowace lita ba a kwanan baya.

LEADERSHIP Hausa ta bibiyi ra’ayoyin wasu ‘Yan Nijeriya a kafafen sadarwa daban-daban domin jin halin da suke ciki inda galibi suka yi bayanin cewa a gaskiya suna jin jiki.

Bashir Bello ya bayyana cewa, “Ga talauci ga yunwa ga tsadar rayuwa ga kuncin rayuwa ga rashin tsaro. Wai ni Allah! Ina ake so talaka ya sa kansa ne? Allah ya kawo mana karshan wannan lamarin a kasar nan.”
Haka zalika, Aliyu Umar ya fadi cewa, “Allah ya kara shiga lamuranmu. Amma duk ranar talaka ya fara bore a Nijeriya mai tare shi sai Allah.”

Labarai Masu Nasaba

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Shi ma da yake bayyana nashi ra’ayin, Nuhu Mika’il ya bayyana cewa, “Masu mulki ku ji tsoran boren talakawan Nijeriya. Domin duk ranar da talakawan Nijeriya suka yi bore, sai dai masu mulki su yi hijira.”

A nasa ra’ayin kuwa, Muhammad Sani ya bayyana cewa, “Duk wannan ce-ce-ku-ce da ake yi kan tsadar rayuwa ba na kallon hakan mafita, domin tsadar rayuwar tana wa wasu fa’ida saboda burinsu kenan. Allah za mu roka mafita tare da kyautata halayyenmu.”

Da yake bayyana ra’ayinsa, Hamza Unikue Hamza ya bayyana cewa, “Talakawan Nijeriya suna ganin hisabin duniya kam. Allah Ubangiji ya saukaka mana tsadar rayuwa da muke ciki, Amin.”

A lokacin da yake bayyana nasa ra’ayin, wani dan kasuwa, Malam Kabir Garba ya bayyana cewa, “’Yan Arewa dole ne ku bai wa Jagaba uzurin kamar yadda kuka bai wa Muhammadu Buhari, saboda shi gyaran targade dama haka yake zuwa da tsananin zafi.”

Ga dukkan alamu dai mafi yawancin ‘yan Nijeriya ba su ji dadin wannan tashin gwauron zabon da farashin man fetur da kayan masarufi ke ci gaba da yi ba, musamman yadda ake ci gaba da samun matalauta a kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Waje Da Kamfanonin Sin Suka Zuba A Kasashen Waje Ya Karu A Watanni Shida Na Farkon Bana

Next Post

Yadda Aka Gudanar Da Walimar Karrama Tsohon Shugaban NIS Isah Idris Jere

Related

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

8 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

9 hours ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

11 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

12 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

13 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

15 hours ago
Next Post
Yadda Aka Gudanar Da Walimar Karrama Tsohon Shugaban NIS Isah Idris Jere

Yadda Aka Gudanar Da Walimar Karrama Tsohon Shugaban NIS Isah Idris Jere

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.