ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Fetur Da Abinci: Gaskiya Muna Jin Jiki, In Ji ‘Yan Nijeriya

•Tsadar Kayan Masarufi Ta Karu Zuwa Kashi 22.7 Cikin 100

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tsadar Fetur

‘Yan Nijeriya sun shiga halin taraddudi a wannan makon yayin da farashin man fetur da kayayyakin masarufi suka yi tashin gwauron zabi.

Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta bayyana cewa hauhawan farashin kayan abinci a watan Yunin 2023, ya kai kashi 22.79 a cikin dari idan aka kwatanta da na watan Mayun 2023, da ya kasance da kashi 22.41 a cikin dari.
Wannan na kunshe a cikin rahoton farashin kayan abinci (CPI) na wata-wata da NBS ta fitar a makon nan. A cewar rahoton NBS, karin farashin ya kai kashi 0.38 a cikin dari, inda rahoton ya yi karin hasken cewa idan aka duba mizanin shekara-shekara, za a ga cewa farashin ya karu ne da kashi 4.19 a cikin dari, idan aka kwatanta da wanda aka samu a watan Yunin 2022 da bai wuce kashi 18.60 a cikin dari.
NBS ta ce, an samu karuwar farashin ne a kan kayayyaki kamar su, man girki, burodi, hatsi, dankali, doya, kifi, nama, kwai, kayan lambu da sauransu.

  • Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Kai Kashi 21.82 – NBS

Sauran harkokin da aka samu karin farashin su ne, sufuri, iskar gas, kayan gyaran ababen hawa, kiwon lafiya da bakin mai.
Sai dai ‘Yan Nijeriya ba su gama jimamin tsadar farashin kayan masarufin ba, kwatsam sai ga sanarwar karin farashin litar man fetur daga Naira 539 zuwa naira 617 a Babban Birnin Tarayya Abuja.
Ana kyautata zaton karin farashin man ba zai rasa nasaba da batun da ‘yan kasuwar man suka yi cewa farashin na iya kaiwa Naira 700 kan kowace lita ba a kwanan baya.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP Hausa ta bibiyi ra’ayoyin wasu ‘Yan Nijeriya a kafafen sadarwa daban-daban domin jin halin da suke ciki inda galibi suka yi bayanin cewa a gaskiya suna jin jiki.

Bashir Bello ya bayyana cewa, “Ga talauci ga yunwa ga tsadar rayuwa ga kuncin rayuwa ga rashin tsaro. Wai ni Allah! Ina ake so talaka ya sa kansa ne? Allah ya kawo mana karshan wannan lamarin a kasar nan.”
Haka zalika, Aliyu Umar ya fadi cewa, “Allah ya kara shiga lamuranmu. Amma duk ranar talaka ya fara bore a Nijeriya mai tare shi sai Allah.”

LABARAI MASU NASABA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

Shi ma da yake bayyana nashi ra’ayin, Nuhu Mika’il ya bayyana cewa, “Masu mulki ku ji tsoran boren talakawan Nijeriya. Domin duk ranar da talakawan Nijeriya suka yi bore, sai dai masu mulki su yi hijira.”

A nasa ra’ayin kuwa, Muhammad Sani ya bayyana cewa, “Duk wannan ce-ce-ku-ce da ake yi kan tsadar rayuwa ba na kallon hakan mafita, domin tsadar rayuwar tana wa wasu fa’ida saboda burinsu kenan. Allah za mu roka mafita tare da kyautata halayyenmu.”

Da yake bayyana ra’ayinsa, Hamza Unikue Hamza ya bayyana cewa, “Talakawan Nijeriya suna ganin hisabin duniya kam. Allah Ubangiji ya saukaka mana tsadar rayuwa da muke ciki, Amin.”

A lokacin da yake bayyana nasa ra’ayin, wani dan kasuwa, Malam Kabir Garba ya bayyana cewa, “’Yan Arewa dole ne ku bai wa Jagaba uzurin kamar yadda kuka bai wa Muhammadu Buhari, saboda shi gyaran targade dama haka yake zuwa da tsananin zafi.”

Ga dukkan alamu dai mafi yawancin ‘yan Nijeriya ba su ji dadin wannan tashin gwauron zabon da farashin man fetur da kayan masarufi ke ci gaba da yi ba, musamman yadda ake ci gaba da samun matalauta a kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Yadda Aka Gudanar Da Walimar Karrama Tsohon Shugaban NIS Isah Idris Jere

Yadda Aka Gudanar Da Walimar Karrama Tsohon Shugaban NIS Isah Idris Jere

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.