ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Fetur Da Abinci: Gaskiya Muna Jin Jiki, In Ji ‘Yan Nijeriya

•Tsadar Kayan Masarufi Ta Karu Zuwa Kashi 22.7 Cikin 100

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tsadar Fetur

‘Yan Nijeriya sun shiga halin taraddudi a wannan makon yayin da farashin man fetur da kayayyakin masarufi suka yi tashin gwauron zabi.

Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta bayyana cewa hauhawan farashin kayan abinci a watan Yunin 2023, ya kai kashi 22.79 a cikin dari idan aka kwatanta da na watan Mayun 2023, da ya kasance da kashi 22.41 a cikin dari.
Wannan na kunshe a cikin rahoton farashin kayan abinci (CPI) na wata-wata da NBS ta fitar a makon nan. A cewar rahoton NBS, karin farashin ya kai kashi 0.38 a cikin dari, inda rahoton ya yi karin hasken cewa idan aka duba mizanin shekara-shekara, za a ga cewa farashin ya karu ne da kashi 4.19 a cikin dari, idan aka kwatanta da wanda aka samu a watan Yunin 2022 da bai wuce kashi 18.60 a cikin dari.
NBS ta ce, an samu karuwar farashin ne a kan kayayyaki kamar su, man girki, burodi, hatsi, dankali, doya, kifi, nama, kwai, kayan lambu da sauransu.

  • Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Kai Kashi 21.82 – NBS

Sauran harkokin da aka samu karin farashin su ne, sufuri, iskar gas, kayan gyaran ababen hawa, kiwon lafiya da bakin mai.
Sai dai ‘Yan Nijeriya ba su gama jimamin tsadar farashin kayan masarufin ba, kwatsam sai ga sanarwar karin farashin litar man fetur daga Naira 539 zuwa naira 617 a Babban Birnin Tarayya Abuja.
Ana kyautata zaton karin farashin man ba zai rasa nasaba da batun da ‘yan kasuwar man suka yi cewa farashin na iya kaiwa Naira 700 kan kowace lita ba a kwanan baya.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP Hausa ta bibiyi ra’ayoyin wasu ‘Yan Nijeriya a kafafen sadarwa daban-daban domin jin halin da suke ciki inda galibi suka yi bayanin cewa a gaskiya suna jin jiki.

Bashir Bello ya bayyana cewa, “Ga talauci ga yunwa ga tsadar rayuwa ga kuncin rayuwa ga rashin tsaro. Wai ni Allah! Ina ake so talaka ya sa kansa ne? Allah ya kawo mana karshan wannan lamarin a kasar nan.”
Haka zalika, Aliyu Umar ya fadi cewa, “Allah ya kara shiga lamuranmu. Amma duk ranar talaka ya fara bore a Nijeriya mai tare shi sai Allah.”

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

Shi ma da yake bayyana nashi ra’ayin, Nuhu Mika’il ya bayyana cewa, “Masu mulki ku ji tsoran boren talakawan Nijeriya. Domin duk ranar da talakawan Nijeriya suka yi bore, sai dai masu mulki su yi hijira.”

A nasa ra’ayin kuwa, Muhammad Sani ya bayyana cewa, “Duk wannan ce-ce-ku-ce da ake yi kan tsadar rayuwa ba na kallon hakan mafita, domin tsadar rayuwar tana wa wasu fa’ida saboda burinsu kenan. Allah za mu roka mafita tare da kyautata halayyenmu.”

Da yake bayyana ra’ayinsa, Hamza Unikue Hamza ya bayyana cewa, “Talakawan Nijeriya suna ganin hisabin duniya kam. Allah Ubangiji ya saukaka mana tsadar rayuwa da muke ciki, Amin.”

A lokacin da yake bayyana nasa ra’ayin, wani dan kasuwa, Malam Kabir Garba ya bayyana cewa, “’Yan Arewa dole ne ku bai wa Jagaba uzurin kamar yadda kuka bai wa Muhammadu Buhari, saboda shi gyaran targade dama haka yake zuwa da tsananin zafi.”

Ga dukkan alamu dai mafi yawancin ‘yan Nijeriya ba su ji dadin wannan tashin gwauron zabon da farashin man fetur da kayan masarufi ke ci gaba da yi ba, musamman yadda ake ci gaba da samun matalauta a kasar.

Tsadar Fetur
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
Labarai

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana
Labarai

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Next Post
Yadda Aka Gudanar Da Walimar Karrama Tsohon Shugaban NIS Isah Idris Jere

Yadda Aka Gudanar Da Walimar Karrama Tsohon Shugaban NIS Isah Idris Jere

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.