ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Nijeriya Da BRICS+: Idan Zamani Ya Dinka Riga…

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
BRICS

”Idan zamani ya dinka riga, ya kamata a saka.” Wannan magana ta nuna hikimar Hausawa ta kokarin tafiya tare da zamani a ko yaushe. Sa’an nan yadda kasar Najeriya ta shiga tsarin BRICS+ a matsayin abokiyar hulda a kwanan nan, shi ma ya nuna hikimar tafiya tare da yanayin zamani sosai.

Ko mene ne yanayin zamani da Najeriya ta tafi da shi? Shi ne haskakawar tauraron kasashe masu tasowa, ko kuma “Global South” a bakin Turawa, a duniya.

  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu
  • Ba Ma Cikin Waɗanda Suka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga – Gwamnatin Katsina

Mun san rikicin hada-hadar kudi da ya abku a shekarar 2008 ya sa dimbin kasashe masu sukuni fuskantar matsalar koma bayan tattalin arzikinsu. Tun daga lokacin, wasu kasashen da tattalin arzikinsu ke tasowa cikin sauri, ciki har da kasar Sin, sannu a hankali suka fara zama wadanda ke samar da mafi yawan karuwar tattalin arzikin duniya. Daga bisani, wadannan kasashe sun yi amfani da tsarin hadin gwiwa na BRICS wajen wanzar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a duniya, da taimakon sauran kasashe masu tasowa wajen zamanantarwa, ta hanyar hadin gwiwa a fannonin cinikayya da masana’antu. A lokacin da ake aiwatar da wannan mataki, kasashe masu tasowa sun fara taka muhimmiyar rawa a fannin kulawa da al’amuran duniya, inda suke kokarin yin garambawul da zai tabbatar da adalci, da daidaituwa, gami da wakiltar mafi yawan kasashe.

ADVERTISEMENT

Yanzu kasar Najeriya ita ma ta shiga tsarin BRICS+, kuma hakan zai kara karfin tsarin hadin gwiwa na BRICS+, ganin yadda yawan al’ummarsa zai kai kaso 54.6% na daukacin al’ummar duniya, kana GDPnsa zai kai kaso 42.2% na adadin na duniya. Hakan zai sa kasashen BRICS da abokan huldarsu samun damar karfafa wa kasashe masu tasowa ikon fada-a-ji, da inganta wakilcinsu a hukumomin duniya, gami da sanya tsarin hada-hadar kudi na duniya ya dace da yanayin ci gaban kasashen da tattalin arzikinsu ke kan hanyar tasowa.

Sa’an nan a nata bangaren, Najeriya za ta samu alfanu a fannoni daban daban, ta hanyar zama abokiyar huldar kasashen BRICS, wadanda a kalla suka kunshi wadannan bangarori: Wato na farko, bisa tsarin gudanar da ciniki da kudin kashin kai na ko wace kasa da kasashen BRICS ke kokarin yayatawa, Najeriya za ta iya aiwatar da karin cinikin waje da kudinta na Naira, don rage dogaro kan dalar Amurka. Ta haka, kasar za ta samu damar sasanta matsalar karancin kudin musaya, wadda kan haddasa matsalar tafiyar hawainiya ga ci gaban tattalin arziki a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

Na biyu, nan gaba Najeriya tana da damar samun bashi daga bankin raya kasa na NDB, da tsarin samar da kudi cikin gaggawa na CRA, duk a karkashin tsarin BRICS, don tallafa wa ayyukanta na gina kayayyakin more rayuwa, da dai sauransu.

Na uku, a matsayinta na babbar kasa mai dimbin al’umma da karfin tattalin arizki ta nahiyar Afirka, Najeriya na neman zama mai fada-a-ji a Majalisar Dinkin Duniya da sauran hukumomi na duniya. To, kasar tana da damar cika burinta a wannan fanni, bisa goyon bayan da za ta iya samu daga tsarin BRICS+.

Na hudu, idan an yi nazari tare da hangen nesa, to, za a ga yadda wasu abubuwan da tsarin BRICS+ ya kunsa, irinsu kasancewar mabambantan al’adu tare cikin daidaito, da cudanya tsakaninsu don neman koyi da juna, za su taimaki Najeriya, a kokarinta na lalubo hanyar raya kai, wadda za ta dace da ainihin yanayin da kasar ke ciki. Wannan shi ne dalilin da ya sa ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta furta cewa, zama abokiyar huldar kasashen BRICS “wani gwaji ne mafi kyau a kokarin kasar na tabbatar da tsare-tsaren raya kasa na kashin kanta”. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

December 17, 2025
Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing

December 16, 2025
Next Post
Fashewar Tankar Mai A Suleja: An Kai Mutum 20 Manyan Asibitocin Abuja Don Samun Kulawa Ta Musamman

Fashewar Tankar Mai A Suleja: An Kai Mutum 20 Manyan Asibitocin Abuja Don Samun Kulawa Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.