• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Nijeriya Da BRICS+: Idan Zamani Ya Dinka Riga…

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
BRICS

”Idan zamani ya dinka riga, ya kamata a saka.” Wannan magana ta nuna hikimar Hausawa ta kokarin tafiya tare da zamani a ko yaushe. Sa’an nan yadda kasar Najeriya ta shiga tsarin BRICS+ a matsayin abokiyar hulda a kwanan nan, shi ma ya nuna hikimar tafiya tare da yanayin zamani sosai.

Ko mene ne yanayin zamani da Najeriya ta tafi da shi? Shi ne haskakawar tauraron kasashe masu tasowa, ko kuma “Global South” a bakin Turawa, a duniya.

  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu
  • Ba Ma Cikin Waɗanda Suka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga – Gwamnatin Katsina

Mun san rikicin hada-hadar kudi da ya abku a shekarar 2008 ya sa dimbin kasashe masu sukuni fuskantar matsalar koma bayan tattalin arzikinsu. Tun daga lokacin, wasu kasashen da tattalin arzikinsu ke tasowa cikin sauri, ciki har da kasar Sin, sannu a hankali suka fara zama wadanda ke samar da mafi yawan karuwar tattalin arzikin duniya. Daga bisani, wadannan kasashe sun yi amfani da tsarin hadin gwiwa na BRICS wajen wanzar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a duniya, da taimakon sauran kasashe masu tasowa wajen zamanantarwa, ta hanyar hadin gwiwa a fannonin cinikayya da masana’antu. A lokacin da ake aiwatar da wannan mataki, kasashe masu tasowa sun fara taka muhimmiyar rawa a fannin kulawa da al’amuran duniya, inda suke kokarin yin garambawul da zai tabbatar da adalci, da daidaituwa, gami da wakiltar mafi yawan kasashe.

Yanzu kasar Najeriya ita ma ta shiga tsarin BRICS+, kuma hakan zai kara karfin tsarin hadin gwiwa na BRICS+, ganin yadda yawan al’ummarsa zai kai kaso 54.6% na daukacin al’ummar duniya, kana GDPnsa zai kai kaso 42.2% na adadin na duniya. Hakan zai sa kasashen BRICS da abokan huldarsu samun damar karfafa wa kasashe masu tasowa ikon fada-a-ji, da inganta wakilcinsu a hukumomin duniya, gami da sanya tsarin hada-hadar kudi na duniya ya dace da yanayin ci gaban kasashen da tattalin arzikinsu ke kan hanyar tasowa.

Sa’an nan a nata bangaren, Najeriya za ta samu alfanu a fannoni daban daban, ta hanyar zama abokiyar huldar kasashen BRICS, wadanda a kalla suka kunshi wadannan bangarori: Wato na farko, bisa tsarin gudanar da ciniki da kudin kashin kai na ko wace kasa da kasashen BRICS ke kokarin yayatawa, Najeriya za ta iya aiwatar da karin cinikin waje da kudinta na Naira, don rage dogaro kan dalar Amurka. Ta haka, kasar za ta samu damar sasanta matsalar karancin kudin musaya, wadda kan haddasa matsalar tafiyar hawainiya ga ci gaban tattalin arziki a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Na biyu, nan gaba Najeriya tana da damar samun bashi daga bankin raya kasa na NDB, da tsarin samar da kudi cikin gaggawa na CRA, duk a karkashin tsarin BRICS, don tallafa wa ayyukanta na gina kayayyakin more rayuwa, da dai sauransu.

Na uku, a matsayinta na babbar kasa mai dimbin al’umma da karfin tattalin arizki ta nahiyar Afirka, Najeriya na neman zama mai fada-a-ji a Majalisar Dinkin Duniya da sauran hukumomi na duniya. To, kasar tana da damar cika burinta a wannan fanni, bisa goyon bayan da za ta iya samu daga tsarin BRICS+.

Na hudu, idan an yi nazari tare da hangen nesa, to, za a ga yadda wasu abubuwan da tsarin BRICS+ ya kunsa, irinsu kasancewar mabambantan al’adu tare cikin daidaito, da cudanya tsakaninsu don neman koyi da juna, za su taimaki Najeriya, a kokarinta na lalubo hanyar raya kai, wadda za ta dace da ainihin yanayin da kasar ke ciki. Wannan shi ne dalilin da ya sa ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta furta cewa, zama abokiyar huldar kasashen BRICS “wani gwaji ne mafi kyau a kokarin kasar na tabbatar da tsare-tsaren raya kasa na kashin kanta”. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Next Post
Fashewar Tankar Mai A Suleja: An Kai Mutum 20 Manyan Asibitocin Abuja Don Samun Kulawa Ta Musamman

Fashewar Tankar Mai A Suleja: An Kai Mutum 20 Manyan Asibitocin Abuja Don Samun Kulawa Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa 

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa 

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.