• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsantseni Da Gudun Duniya Na Annabi S.A.W (2)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
2 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Tsantseni Da Gudun Duniya Na Annabi S.A.W (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sayyada A’isha ta ce, mu da muke Iyalan gidan Manzon Allah (SAW) amma mukan zama wata daya ba mu kunna wutar girki ba sai dai Dabino da Ruwa.

An karba daga Abdurrahman bin Aufin, yana cewa, Annabi (SAW) ya rasu amma da shi da Iyalan Gidansa ba su koshi ba daga Gurasar Sha’ir. Wannan Hadisi ne mai tsawo kuma wanda ya fada wannan Hadisi yana daga cikin masu kudin garin Madina. Ana cewa, da Usman bin Affan da Abdurrahman bin Aufin, kusan rabin kudin duniya, yana hannunsu.

  • Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Gudanar Da Maulidin Manzon Allah (SAW) Na Bana
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Kama Kwale-kwale Da Muggan Kwayoyin Miliyan N200 A Legas

Rabon gadon dukiyar Abdulrrahman bin Aufin, abun mamaki ne, wata daga cikin matansa wacce ya rabu da ita da dadewa, sai da aka ba ta Dinari Dubu Tamanin, bayan wasiyyar da ya bari na raba wani kaso na cikin dukiyarshi amma sai da aka bar dukiya mai yawa. Da aka gama rabon dukiyar, sai Sayyadina Usman ya tambayi Sahabbai cewa, me za ku fada game da dukiyar Abdurrahman bin Aufin? Sai Abu Zarrin ya ce, ai wannan wani mutum ne da ya gama cinye Lahirarsa, sai aka tambaye shi, me ya sa za ka fada hakan? Wannan mutum ne Bawan Allah, sai ya ce, mutumin kirki ne zai tara dukiya kamar haka! Abdurrahman bin Aufin, wata rana ya yi Azumi, lokacin bude baki sai aka kawo masa kwanon nau’ukan nama da abinci kala-kala, nan take sai ya tuna rayuwar Manzon Allah (SAW), sai ya fashe da Kuka, ya ce a dauke, “Annabi (SAW) ya rasu bai ci irin wadannan abubuwa ba”. Wannan Tawadu’u ne ya sa ya fadi maganar da muka ambato muku a baya.

Abdurrahman bin Aufin, kasaitaccen mai kudi ne, ya kula da Matan Annabi (SAW) da Sahabbai musammam ‘Yan Badr (Albashi ya ware wa ‘Yan Badr).

An Karbo Hadisi daga Sayyada A’isha da Abi Umamata da Abdullahi bin Abbas suka ce “Manzon Allah (SAW) da shi da Iyalinsa, suna jera Kwanaki ba su samu abincin Dare ba”.

Labarai Masu Nasaba

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

An karbo Hadisi daga Anas bin Malik ya ce “Manzon Allah (SAW) bai taba cin Abinci a kan Teburi ko Filet ba, ba a taba masa gurasa ba wacce aka cire tsakinta ba” – Amma wannan dama ba Al’adar Larabawa ba ce, Turawa da Mutanen Farisa su suke da wannan Al’ada. Anas bin Malik, albarkar Addu’ar Manzon Allah (SAW) akansa, bayan rasuwarsa, da cebur ake diban zinari wajen rabon gadonsa. Al’adar Sahabbai ce ko kuma Muridai, za ka ga kudi ko dukiyar da Allah ya ke mallaka musu, sai ka ga kaman Shehunansu ba su mallaki irin wannan dukiya ba, don haka, in za su ba da labari, sai su ce, Annabi bai ci abinci iri kaza ba.

Anas ya kara da cewa, “ba a taba wa Annabi gurasa wacce aka cire dusarta ba,”. Ma’ana dai, Annabi (SAW) ba mai cin abinci ba ne irin ta koyaushe ba ko kuma ciki-makabarta (komai sai an ci).

An karbi Hadisi daga Sayyada A’isha ta ce “Shimfidar Annabi (SAW) wacce yake kwana a kanta, fata ce jemammiya da aka tsara ta kamar buhu da za a iya dura abu a ciki, Algararar Dabino ce aka dura a cikin fatar”. Ita kuma Sayyada Hafsatu, matar Annabi (SAW), cewa ta yi “Shimfidar Annabi (SAW) ta cikin dakinsa wacce yake bacci a kanta, Bargo ne aka rubanya shi biyu”, wani dare sai muka rubanya shi hudu, yayin da Annabi (SAW) ya wayi gari, sai ya tambaya wacce irin Shimfida aka yi masa, Sayyada Hafsatu ta ce, Shimfidarka ce amma mun rubanya ta hudu, sai Annabi (SAW) ya ce a maida ita yadda take sabida jiya bai samu damar tashin dare ba, taushinsa ya hana ni Sallah”. Manzon Allah ya kasance wani lokaci kuma yana kwanciya a kan gado wanda aka saka shi da igiyar Kaba, har igiyar kabar ta yi zane a jikin kirjinsa.

Sayyada A’isha ta ce, “Cikin Manzon Allah (SAW) bai taba cika ba don koshi”, Malamai suka ce, Sayyada tana nufin cewa, Annabi (SAW) bai taba makare cikinshi da abinci ba irin wanda za ka ga mutum sabida ya ci da yawa da kyar yake numfashi. Annabi (SAW) Balarabe ne, Larabawa suna amfani da Madara, ita kuma Abinci ce mai zaman kanta don haka, tsarin cin abincin Annabi (SAW) ba zai yi daidai da sauran al’ummatai ba. Sa’adu bin Ubadata, shi kadai ya bai wa Annabi (SAW) Rakuma 45 wadanda ya raba wa matansa don tatsar Nono.

“Manzon Allah (SAW) bai taba bayyana bukatarsa ga wani ba sai Ubangijinsa” – Malamai suka yi sharhi da cewa, Annabi (SAW) ba ya roko amma yana da ‘yan sirri, wadanda yake sirri da su. Annabi (SAW) yakan nemi a biya bukatar wasu a wurin sahabbansa amma ba a kanshi ba, don haka, aka rahoto yana cin bashi, har ya rasu Silkensa yana wurin jingina.

Annabi (SAW) ya kasance ya fi son Talauci daga wadata, wannan Tawadu’u ne nasa, kuma bai hana ya koyar da Addu’ar tsira daga Talauci ba inda yake cewa, Talauci ya kusa zama Kafirci, ya bayar da Addu’a cewa, “duk mai karanta ‘Iza waka’ ba zai yi karkaf ba”.

Zuhudun Annabi (SAW), zuhudun mai kudi ne kuma bai dora wa kowa ba, ya ba wa iyalinsa kowacce abincin shekara.

Duk mai son Mushahada da Hadara ko aiki da Aljanu dole sai ransa ta fi jikinsa nauyi, kuma ana iya yin hakan ne ta hanyar takaita ciye-ciye. Idanuwa, jikkuna suke kallo (Basaru), ita kuma Rai, Ruhi take kallo (Basira). Basira ita ce ke kallon abin da ba a gani, don haka, sai rai ta yi Ma’arifa ta yi Ibada ta narke, ta fi karfin jiki, ita ke sarrafa sha’awoyin Dan’adam guda biyar: Gani, Ji, Dandano, Shaka da Shafa. Da irin wannan ne Rai za ta fara ganin abin da ba a gani, har ta koma gani ba da Ido ba, magana ba da baki ba,  Shaka ba da Hanci ba, Ji ba da Kunne ba, gane taushi ko taurin abu ba tare da an shafa ba. Annabi (SAW), duk da cewa, shi Annabi ne, Allah ya ba shi duk wannan amma sai da ya dinga shiga Kogon Hira yana Ibada – kogon da aka ce akwai abubuwa masu cutarwa.

Annabi (SAW) ya kasance yakan wuni bai ci abinci ba, haka zai ta juye-juye a kan shimfida sabida yunwa amma hakan ba zai hana shi tashi da Azumi gobe ba.

Amma Alhamdulillah… duk wannan, Annabi (SAW) ya zaba ne sabida kankan da kai ga Allah don haka, ya hana kowa ya yi koyi da shi a wannan bangare.

Sayyada A’isha ta ce, na kasance ina yi wa Annabi (SAW) kuka don jinkai game da halin da nake ganinshi amma haka ya so, wani lokacin har sai na shafa cikinsa sabida halin da cikin ya shiga na daga yunwa, sai na fada masa, raina fansa a gare ka, me ya sa ko abin da za ka ci ba za ka tambaya ba? Tun da ba ka son mai yawa. Sai Annabi (SAW) ya ce min, ya ke A’isha! Wai meye ya hada ni da Duniya ne? Abin da nake tsoro, ‘yan’uwana, Annabawa Ulul’azmi (Annabi Nuhu, Ibrahim, Musa da Isa), ma’abota kokari, sun yi juriya a bisa abin da yafi wannan halin da nake ciki na tsanani kuma suka shude a kan haka, suka tafi wurin Ubangijinsu a haka, Allah ya girmama makomarsu, so kike in je in sami Ubangijina ina jin kunya ban yi komai ba? Sabida ni kawai dan gata ne?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MadinaMakkahManzon Allah S.A.WMusulunci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

Next Post

Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa

Related

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

2 weeks ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

3 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

4 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

1 month ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)

1 month ago
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah
Dausayin Musulunci

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

2 months ago
Next Post
Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa

Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.