• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Tsaro: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An fara gudanar da wani muhimmin taro na masu ruwa da tsaki a harkar tsaro, laifuffuka da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi, wanda Majalisar Ɗinkin Duniya ta shirya a Jihar Zamfara.

Taron, wanda aka fara shi Litinin ɗin nan a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau, ofishin kula da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da laifuffuka na Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Nijeriya ne ya shirya shi.

Mai magana da yawun Gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu Litinin ɗin nan a Gusau, ya bayyana cewa taron, wani shiri ne fayyacewa da lalubo hanyoyin mayar da martani game da matsalolin harkar tsaro da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi.

  • Yajin Aiki Ya Hana Sauraren Shari’ar Sarakunan Kano

 

Sulaiman Bala ya ƙara da cewa, wata tawagar Majalisar Ɗinkin Duniya, ƙarƙashin jagorancin Oliver Stolpe, wanda kuma shi ne wakili a Nijeriya na UNODC, taron zai tattaro masu ruwa da tsaki, inda za su zauna na tsawon kwanaki uku.

Labarai Masu Nasaba

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

Sanarwar ta ce, “A wani muhimmin abu na masu ruwa da tsaki, ofishin kula da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da laifuffuka na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNODC) ya shirya wani taron ƙara wa juna sani na kwana uku a kan harkar tsaro yau a Gusau.

“Taron ya samar da masu ruwa da tsaki na cikin gida, da wasu baƙi daga Majalisar Ɗinkin Duniya, inda za su yi zuzzurfan nazari, samar da hanyoyin magance duk wani yanayi na tsaro, laifuffuka da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a jihar Zamfara.

“Taron ya bayyana ingantattun ayyuka da kuma hanyoyin da za a bi daga ciki da wajen Nijeriya wajen tunkarar waɗannan ƙalubale don samar da wani shiri na haɗin gwiwa.”

A jawabinsa na buɗe taron, Gwamna Lawal ya jaddada cewa, ƙwaƙƙwarar tawaga ta masana daga Majalisar Ɗinkin Duniya sun nuna aniyarsu ta haɗin gwiwa wajen magance ƙalubalen da ke addabar Zamfara, da suka haɗa da ’yan bindiga da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi.

Ya ce, “Kwanan nan na ziyarci Majalisar Ɗinkin Duniya domin neman shiga tsakani don magance wasu matsalolin da muke fuskanta, inda na samu kyakkyawar alaƙa da Amina J. Mohammed, mataimakiyar Sakatare Janar ta Majalisar Ɗinkin Duniya da kuma sauran ɓangarorin da take jagoranta ciki har da shugaban ofishin kula da miyagun ƙwayoyi da sauran laifuka.

“Saboda haka, wannan taron ƙara wa juna sani shaida ne na himmar da Majalisar Ɗinkin Duniya ke da shi na cika alƙawuran da ta ɗauka don taimaka mana mu ƙara fahimtar yadda za mu magance ƙalubalen da mu ke fuskanta. Muna matuƙar godiya.

“Sama da shekaru goma, Zamfara tana fama da waɗannan matsalolin da ke kawo cikas ga tsaro da zaman lafiyar al’ummarmu da kuma kawo cikas ga ci gaban zamantakewa da tattalin arziki. Don haka gwamnatina ta ɗauki wannan ziyara da taron bita da muhimmanci, domin sakamakon zai nuna yadda manufofinmu za su kasance wajen dabarun yaƙi da waɗannan ƙalubale.

“Na yi farin cikin ganin cewa za a tattauna batutuwa da dama yayin taron.

“Waɗannan sun haɗa da bayyanar da tushen matsalolin rashin tsaro da aikata laifuka a jihar, kamar garkuwa da mutane, satar shanu, haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba, da rikicin ƙabilanci, rawar da jami’an tsaro daban-daban na jihohi da cibiyoyin gargajiya suke takawa wajen yaƙar matsalolin, tallafin Majalisar Ɗinkin Duniya ga ƙarfafa shari’a a aikata laifuka.

“Hanyoyi da yanayin da ke haifar wa al’umma shaye-shayen miyagun kwayoyi a Jihar Zamfara da wanda za a bi wajen rigakafin shan muggan ƙwayoyi da sauran muhimman batutuwa, duk an shirya su don tattaunawa a wannan taro.

“Ina kira ga mahalarta taron da su yi amfani da wannan damar kuma su bada himma don cin gajiyar ayyukan. Ya kamata ku saurara, ku koya, kuma ku bada gudunmawa mai inganci.

“A ƙarshe, ina fatan dukkanin mahalarta taron za su kasance masu amfanar al’umma. Kamar yadda na bayyana, shawarwarin da aka samar a nan za su kasance masu muhimmanci wajen tsara dabarunmu da ayyukanmu don magance matsalolin da mu ke fuskanta.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dauda LawalGusauGwamnaJihar ZamfaraTsaroZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mafarkin Amurka Ya Rube Saboda Tsanantar Gibin Dake Tsakanin Matalauta Da Masu Arziki  

Next Post

Yajin Aiki: An Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC/TUC, Za A Koma Teburin Sulhu

Related

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu
Manyan Labarai

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

46 minutes ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

4 hours ago
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

15 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

17 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

19 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

21 hours ago
Next Post
Ƙungiyar Ƙwadago Ta NLC Na Zanga-zanga Kan Ƙarin Ƙudin Wutar Lantarki A Nijeriya

Yajin Aiki: An Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC/TUC, Za A Koma Teburin Sulhu

LABARAI MASU NASABA

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

July 13, 2025
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

July 13, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

July 13, 2025
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

July 13, 2025
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.