• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Yadda Sojoji Ke Rakiyar Matafiya Tsakanin Gusau Zuwa Dansadau

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Tsaro: Yadda Sojoji Ke Rakiyar Matafiya Tsakanin Gusau Zuwa Dansadau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu rashin zirga-zirgar ababen hawa a kan hanyar Gusau zuwa Dansadau mai matukar hadari a Jihar Zamfara, kamar yadda wata ziyarar gani ido da ta tabbatar.
Ziyarar dai na zuwa ne domin tabbatar da ko matafiya sun daina amfani da hanyar gaba daya sakamakon ci gaba da kai hare-hare, kashe-kashe, da garkuwa da fasinjoji da ‘yan fashin ke yi a yanzu haka da kuma rashin cin gajiyar hanyar saboda kara munana ayyukansu.

Hanyar mai nisan kilomita 110 na daya daga cikin hanyoyin gwamnatin tarayya a fadin kasar nan da ta lalace tare da haifar da wahalhalu masu tsanani da bakin ciki ga dimbin ‘yan Nijeriya.

  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Mali
  • Kasafin 2024: Tinubu Da Shettima Za Su Lakume Naira Biliyan 15.961Wajen Tafiye-tafiye

Arewa PUNCH ta nakalto cewa hanyar mai matukar muhimmanci ta dade a cikin wannan hali na na lalacewa duk da muhimmancinta na zirga-zirgar ta fuskar tattalin arziki, amma har yanzu ba a dauki matakai na gyara ta ba.

Titin da gwamnatin farar hula tun ta Jamhuriya ta biyu ta mulkin Tsohon Shugaban Kasa Shehu Shagari ta gina a shekarar 1982 ba a taba gyara ta ba tun daga wancan lokaci har zuwa shekarar 2002 lokacin da gwamnan farar hula na farko a Jihar Zamfara, Alhaji Ahmed Sani Yarima ya ba da kwangilar gyaran kananan hukumomin.

Akwai garuruwa da kauyuka da dama a kan hanyar Gusau zuwa Zamfara domin sama da kashi 30 cikin 100 na kayan abincin da jama’ar jihar ke nomawa mazauna wannan yanki ne suke samarwa.

Labarai Masu Nasaba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

Ziyarar da wakilinmu ya kai a titin ya nuna cewa gaba daya kwaltar ta lalace tamkar ba a taba yin ta ba gaba daya.

Majiya mai tushe ta shaida cewa kafin yanzu hanyar ta zama tarkon ajali sakamakon manyan ramuka, da dimbin ‘yan fashi da makami da ke jiran su ga mutane su yi garkuwa da su akan wannan hanya da ta taso daga Zamfara zuwa jihohin Kebbi da Kaduna.

Rahotanni sun ce an yi asarar rayuka da dama a kan hanyar gami da yin garkuwa da dubban mutane, kuma an biya miliyoyin Naira a matsayin kudin fansa ga masu garkuwa da mutane ta hanyar alaka da wadanda abin ya shafa, lamarin da ya tilasta wa al’ummar jihar daina bi ta hanyar in dai ba tare da rakiyar jami’an tsaron soji ba.

Wani mazaunin yankin mai suna Musa Garba ya shaida cewa dole ne masu ababen hawa da ke son tafiya kan titin su rika tafiya a kungiyance bayan sun samu amincewar jami’an soji na yi musu rakiya a ayarin motocin.

Garba ya ci gaba da bayanin cewa, yawan masu ababen hawa da za su bi wannan hanya mai hatsarin yawanci daga 20 zuwa sama ne wadanda dole ne su tafi da ayarin motocin da ke karkashin tsauraran matakai na rakiyar sojoji da ba su wuce 30 ba da za su ba su kariya idan ‘yan fashi sun yi kokarin kai musu farmaki.

Ya nanata cewa zai zama kamar wanu kunar bakin wake ne a ce direbobi ko da sun kai biyar ne in suka kuskura suka bi wannan hanya ba tare da rakiyar sojoji ba saboda ’yan fashin sun mamaye yankin baki daya.
A cewarsa, “Zai zama babban ganganci da jawo wa kai bala’i da kisan kai ga duk wanda ya yi yunkurin zuwa garin Dansadau daga Gusau ba tare da jami’an tsaro sun yi masa rakiya ba.

“Yankin wuri ne mai hadari, kuma babu wanda ya taba yunkurin zuwa Dansadau ba tare da jami’an tsaro ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yabawa Kasar Sin Bisa Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Kasashe Masu Tasowa Kan Sauyin Yanayi Yayin Babban Taron Sauyin Yanayi Na MDD

Next Post

Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

Related

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

3 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

5 hours ago
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Labarai

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

7 hours ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

7 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

19 hours ago
Next Post
Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

LABARAI MASU NASABA

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

August 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

August 26, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.