• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Yadda Sojoji Ke Rakiyar Matafiya Tsakanin Gusau Zuwa Dansadau

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Tsaro: Yadda Sojoji Ke Rakiyar Matafiya Tsakanin Gusau Zuwa Dansadau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu rashin zirga-zirgar ababen hawa a kan hanyar Gusau zuwa Dansadau mai matukar hadari a Jihar Zamfara, kamar yadda wata ziyarar gani ido da ta tabbatar.
Ziyarar dai na zuwa ne domin tabbatar da ko matafiya sun daina amfani da hanyar gaba daya sakamakon ci gaba da kai hare-hare, kashe-kashe, da garkuwa da fasinjoji da ‘yan fashin ke yi a yanzu haka da kuma rashin cin gajiyar hanyar saboda kara munana ayyukansu.

Hanyar mai nisan kilomita 110 na daya daga cikin hanyoyin gwamnatin tarayya a fadin kasar nan da ta lalace tare da haifar da wahalhalu masu tsanani da bakin ciki ga dimbin ‘yan Nijeriya.

  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Mali
  • Kasafin 2024: Tinubu Da Shettima Za Su Lakume Naira Biliyan 15.961Wajen Tafiye-tafiye

Arewa PUNCH ta nakalto cewa hanyar mai matukar muhimmanci ta dade a cikin wannan hali na na lalacewa duk da muhimmancinta na zirga-zirgar ta fuskar tattalin arziki, amma har yanzu ba a dauki matakai na gyara ta ba.

Titin da gwamnatin farar hula tun ta Jamhuriya ta biyu ta mulkin Tsohon Shugaban Kasa Shehu Shagari ta gina a shekarar 1982 ba a taba gyara ta ba tun daga wancan lokaci har zuwa shekarar 2002 lokacin da gwamnan farar hula na farko a Jihar Zamfara, Alhaji Ahmed Sani Yarima ya ba da kwangilar gyaran kananan hukumomin.

Akwai garuruwa da kauyuka da dama a kan hanyar Gusau zuwa Zamfara domin sama da kashi 30 cikin 100 na kayan abincin da jama’ar jihar ke nomawa mazauna wannan yanki ne suke samarwa.

Labarai Masu Nasaba

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Ziyarar da wakilinmu ya kai a titin ya nuna cewa gaba daya kwaltar ta lalace tamkar ba a taba yin ta ba gaba daya.

Majiya mai tushe ta shaida cewa kafin yanzu hanyar ta zama tarkon ajali sakamakon manyan ramuka, da dimbin ‘yan fashi da makami da ke jiran su ga mutane su yi garkuwa da su akan wannan hanya da ta taso daga Zamfara zuwa jihohin Kebbi da Kaduna.

Rahotanni sun ce an yi asarar rayuka da dama a kan hanyar gami da yin garkuwa da dubban mutane, kuma an biya miliyoyin Naira a matsayin kudin fansa ga masu garkuwa da mutane ta hanyar alaka da wadanda abin ya shafa, lamarin da ya tilasta wa al’ummar jihar daina bi ta hanyar in dai ba tare da rakiyar jami’an tsaron soji ba.

Wani mazaunin yankin mai suna Musa Garba ya shaida cewa dole ne masu ababen hawa da ke son tafiya kan titin su rika tafiya a kungiyance bayan sun samu amincewar jami’an soji na yi musu rakiya a ayarin motocin.

Garba ya ci gaba da bayanin cewa, yawan masu ababen hawa da za su bi wannan hanya mai hatsarin yawanci daga 20 zuwa sama ne wadanda dole ne su tafi da ayarin motocin da ke karkashin tsauraran matakai na rakiyar sojoji da ba su wuce 30 ba da za su ba su kariya idan ‘yan fashi sun yi kokarin kai musu farmaki.

Ya nanata cewa zai zama kamar wanu kunar bakin wake ne a ce direbobi ko da sun kai biyar ne in suka kuskura suka bi wannan hanya ba tare da rakiyar sojoji ba saboda ’yan fashin sun mamaye yankin baki daya.
A cewarsa, “Zai zama babban ganganci da jawo wa kai bala’i da kisan kai ga duk wanda ya yi yunkurin zuwa garin Dansadau daga Gusau ba tare da jami’an tsaro sun yi masa rakiya ba.

“Yankin wuri ne mai hadari, kuma babu wanda ya taba yunkurin zuwa Dansadau ba tare da jami’an tsaro ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yabawa Kasar Sin Bisa Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Kasashe Masu Tasowa Kan Sauyin Yanayi Yayin Babban Taron Sauyin Yanayi Na MDD

Next Post

Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

Related

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

28 minutes ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

1 hour ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 hour ago
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

2 hours ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 hours ago
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115
Labarai

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

3 hours ago
Next Post
Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

LABARAI MASU NASABA

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

May 31, 2025
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

May 31, 2025
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

May 31, 2025
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

May 31, 2025
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

May 31, 2025
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

May 31, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

May 31, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

May 31, 2025
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.