ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Yadda Sojoji Ke Rakiyar Matafiya Tsakanin Gusau Zuwa Dansadau

by Sulaiman
2 years ago
Dansadau

An samu rashin zirga-zirgar ababen hawa a kan hanyar Gusau zuwa Dansadau mai matukar hadari a Jihar Zamfara, kamar yadda wata ziyarar gani ido da ta tabbatar.
Ziyarar dai na zuwa ne domin tabbatar da ko matafiya sun daina amfani da hanyar gaba daya sakamakon ci gaba da kai hare-hare, kashe-kashe, da garkuwa da fasinjoji da ‘yan fashin ke yi a yanzu haka da kuma rashin cin gajiyar hanyar saboda kara munana ayyukansu.

Hanyar mai nisan kilomita 110 na daya daga cikin hanyoyin gwamnatin tarayya a fadin kasar nan da ta lalace tare da haifar da wahalhalu masu tsanani da bakin ciki ga dimbin ‘yan Nijeriya.

  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Mali
  • Kasafin 2024: Tinubu Da Shettima Za Su Lakume Naira Biliyan 15.961Wajen Tafiye-tafiye

Arewa PUNCH ta nakalto cewa hanyar mai matukar muhimmanci ta dade a cikin wannan hali na na lalacewa duk da muhimmancinta na zirga-zirgar ta fuskar tattalin arziki, amma har yanzu ba a dauki matakai na gyara ta ba.

ADVERTISEMENT

Titin da gwamnatin farar hula tun ta Jamhuriya ta biyu ta mulkin Tsohon Shugaban Kasa Shehu Shagari ta gina a shekarar 1982 ba a taba gyara ta ba tun daga wancan lokaci har zuwa shekarar 2002 lokacin da gwamnan farar hula na farko a Jihar Zamfara, Alhaji Ahmed Sani Yarima ya ba da kwangilar gyaran kananan hukumomin.

Akwai garuruwa da kauyuka da dama a kan hanyar Gusau zuwa Zamfara domin sama da kashi 30 cikin 100 na kayan abincin da jama’ar jihar ke nomawa mazauna wannan yanki ne suke samarwa.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Ziyarar da wakilinmu ya kai a titin ya nuna cewa gaba daya kwaltar ta lalace tamkar ba a taba yin ta ba gaba daya.

Majiya mai tushe ta shaida cewa kafin yanzu hanyar ta zama tarkon ajali sakamakon manyan ramuka, da dimbin ‘yan fashi da makami da ke jiran su ga mutane su yi garkuwa da su akan wannan hanya da ta taso daga Zamfara zuwa jihohin Kebbi da Kaduna.

Rahotanni sun ce an yi asarar rayuka da dama a kan hanyar gami da yin garkuwa da dubban mutane, kuma an biya miliyoyin Naira a matsayin kudin fansa ga masu garkuwa da mutane ta hanyar alaka da wadanda abin ya shafa, lamarin da ya tilasta wa al’ummar jihar daina bi ta hanyar in dai ba tare da rakiyar jami’an tsaron soji ba.

Wani mazaunin yankin mai suna Musa Garba ya shaida cewa dole ne masu ababen hawa da ke son tafiya kan titin su rika tafiya a kungiyance bayan sun samu amincewar jami’an soji na yi musu rakiya a ayarin motocin.

Garba ya ci gaba da bayanin cewa, yawan masu ababen hawa da za su bi wannan hanya mai hatsarin yawanci daga 20 zuwa sama ne wadanda dole ne su tafi da ayarin motocin da ke karkashin tsauraran matakai na rakiyar sojoji da ba su wuce 30 ba da za su ba su kariya idan ‘yan fashi sun yi kokarin kai musu farmaki.

Ya nanata cewa zai zama kamar wanu kunar bakin wake ne a ce direbobi ko da sun kai biyar ne in suka kuskura suka bi wannan hanya ba tare da rakiyar sojoji ba saboda ’yan fashin sun mamaye yankin baki daya.
A cewarsa, “Zai zama babban ganganci da jawo wa kai bala’i da kisan kai ga duk wanda ya yi yunkurin zuwa garin Dansadau daga Gusau ba tare da jami’an tsaro sun yi masa rakiya ba.

“Yankin wuri ne mai hadari, kuma babu wanda ya taba yunkurin zuwa Dansadau ba tare da jami’an tsaro ba.

Dansadau
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.