ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Yadda Sojoji Ke Rakiyar Matafiya Tsakanin Gusau Zuwa Dansadau

by Sulaiman
3 years ago
Dansadau

An samu rashin zirga-zirgar ababen hawa a kan hanyar Gusau zuwa Dansadau mai matukar hadari a Jihar Zamfara, kamar yadda wata ziyarar gani ido da ta tabbatar.
Ziyarar dai na zuwa ne domin tabbatar da ko matafiya sun daina amfani da hanyar gaba daya sakamakon ci gaba da kai hare-hare, kashe-kashe, da garkuwa da fasinjoji da ‘yan fashin ke yi a yanzu haka da kuma rashin cin gajiyar hanyar saboda kara munana ayyukansu.

Hanyar mai nisan kilomita 110 na daya daga cikin hanyoyin gwamnatin tarayya a fadin kasar nan da ta lalace tare da haifar da wahalhalu masu tsanani da bakin ciki ga dimbin ‘yan Nijeriya.

  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Mali
  • Kasafin 2024: Tinubu Da Shettima Za Su Lakume Naira Biliyan 15.961Wajen Tafiye-tafiye

Arewa PUNCH ta nakalto cewa hanyar mai matukar muhimmanci ta dade a cikin wannan hali na na lalacewa duk da muhimmancinta na zirga-zirgar ta fuskar tattalin arziki, amma har yanzu ba a dauki matakai na gyara ta ba.

ADVERTISEMENT

Titin da gwamnatin farar hula tun ta Jamhuriya ta biyu ta mulkin Tsohon Shugaban Kasa Shehu Shagari ta gina a shekarar 1982 ba a taba gyara ta ba tun daga wancan lokaci har zuwa shekarar 2002 lokacin da gwamnan farar hula na farko a Jihar Zamfara, Alhaji Ahmed Sani Yarima ya ba da kwangilar gyaran kananan hukumomin.

Akwai garuruwa da kauyuka da dama a kan hanyar Gusau zuwa Zamfara domin sama da kashi 30 cikin 100 na kayan abincin da jama’ar jihar ke nomawa mazauna wannan yanki ne suke samarwa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Ziyarar da wakilinmu ya kai a titin ya nuna cewa gaba daya kwaltar ta lalace tamkar ba a taba yin ta ba gaba daya.

Majiya mai tushe ta shaida cewa kafin yanzu hanyar ta zama tarkon ajali sakamakon manyan ramuka, da dimbin ‘yan fashi da makami da ke jiran su ga mutane su yi garkuwa da su akan wannan hanya da ta taso daga Zamfara zuwa jihohin Kebbi da Kaduna.

Rahotanni sun ce an yi asarar rayuka da dama a kan hanyar gami da yin garkuwa da dubban mutane, kuma an biya miliyoyin Naira a matsayin kudin fansa ga masu garkuwa da mutane ta hanyar alaka da wadanda abin ya shafa, lamarin da ya tilasta wa al’ummar jihar daina bi ta hanyar in dai ba tare da rakiyar jami’an tsaron soji ba.

Wani mazaunin yankin mai suna Musa Garba ya shaida cewa dole ne masu ababen hawa da ke son tafiya kan titin su rika tafiya a kungiyance bayan sun samu amincewar jami’an soji na yi musu rakiya a ayarin motocin.

Garba ya ci gaba da bayanin cewa, yawan masu ababen hawa da za su bi wannan hanya mai hatsarin yawanci daga 20 zuwa sama ne wadanda dole ne su tafi da ayarin motocin da ke karkashin tsauraran matakai na rakiyar sojoji da ba su wuce 30 ba da za su ba su kariya idan ‘yan fashi sun yi kokarin kai musu farmaki.

Ya nanata cewa zai zama kamar wanu kunar bakin wake ne a ce direbobi ko da sun kai biyar ne in suka kuskura suka bi wannan hanya ba tare da rakiyar sojoji ba saboda ’yan fashin sun mamaye yankin baki daya.
A cewarsa, “Zai zama babban ganganci da jawo wa kai bala’i da kisan kai ga duk wanda ya yi yunkurin zuwa garin Dansadau daga Gusau ba tare da jami’an tsaro sun yi masa rakiya ba.

“Yankin wuri ne mai hadari, kuma babu wanda ya taba yunkurin zuwa Dansadau ba tare da jami’an tsaro ba.

Dansadau
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.