• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙoƙarin tabbatar da tsaro a iyakokin ƙasa da magance aikata lailufa a iyakokin ƙasar nan, Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta yaye zaratan jami’ai mata masu ɗaukar makami a karon farko da ta horar domin gudanar da aiki na musamman.

Da yake gabatar da jawabi wajen faretin yaye jami’ai matan guda 61 a ranar Juma’a, Shugaban NIS, Isah Idris Jere ya bayyana cewa babban aikin hukumar shi ne samar da tsaro a iyakokin ƙasa domin ƙarfafa tsaron cikin gida.

  • Aisha Buhari Ta Janye Kara Kan Aminu Mohammed Da Ya Ce Ta Yi ‘Bulbul’

 

“A wannan biki na yau, rana ce ta ƙarfafa mana giwa na ƙoƙarin tabbatar da cewa mun tsare iyakokinmu da rayuka da dokiyoyin mutanenmu.

“Hukumar NIS tana da muhimmiyar rawa da take takawa wajen yaƙi da ‘yan ta’adda, laifukan iyakoki da kuma sauran duk wata barazanar tsaro da ke fuskantar ƙasarmu. Domin ƙara ƙarfafa abubuwan da muka daɗe muna gudanarwa na tsawon lokuta, shugabancina ya mayar da hankali ne kan wasu ɓangarori guda uku waɗanda suka hada da: Kula da jin daɗin jami’anmu, gudanar da aiki ba tare da jinkiri ba da kuma inganta aiki irin wanda ake yi a ƙasashen da suka ci gaba a duniya wajen tabbatar da tsare iyakokin ƙasarmu.

Labarai Masu Nasaba

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

“Bisa waɗannan ɓangarori da na lissafo, NIS a ƙarƙashin jagorancina, a ko da yaushe ina muhimmanta kyautata jin daɗin jami’ai da ba su horo a-kai-a-kai ta yadda za su iya fuskantar ƙalubale daban-daban da ƙasarmu ke fuskanta. Za mu ci gaba da bayar da horo da sauran wasu shirye-shirye masu muhimmanci a gida da kumą ƙasashen ƙetare domin ƙara samun ilimi da shirya jami’anmu ta yadda za su iya sauke nauyin da ke kansu.”

Jere ya ƙara da cewa wanna biki wani mataki ne da zai ƙara kwazon aikin hukumar wajen inganta ayyukan jami’a a yankunan da ke fama da rashin tsaro a wurin gudanar da ayyukan ƙasa kamar yadda ake buƙata a lokaci bayan lokaci.

Ya ce waɗannan jami’ai guda 61 dukkansa mata ne waɗanda suka samu horon aiki kan yadda ake sarrafa makamai, kakkaɓo jirgi, tsaron iyakoki, yaƙar ‘yan ta’adda da sauran harkokin bincike da kuma horon sirri.

“Kamar yadda kuke iya gani a yau, waɗannan jami’ai sun nuna zimma tare da aiki kafanɗa da kafaɗa da maza wajen yi wa ƙasarmu hidima. Ina sanar muku da cewa a yanzu haka hukumar ta ɓullo da shirin horar da jami’ai sama da 1000 a makarantar bayar da horo da ke Kano da kuma makarantar horar da jami’an kwastom da ke Goron Dutse a Kano. Muhimmancin bayar da wannan horo shi ne, tabbatar da cewa jami’anmu sun samu ƙwarewa wajen fuskantar matsalolin tsaro da ke addabar ƙasarmu da kuma yin kafaɗa da kafaɗa da takwarorinsu na duniya wajen gudanar da ayyukan shige da fice.

“A wannan gaɓa, ina taya murna ga kwamandan NITSA da ma’aikatansa bisa kafa tarihi a yau, gaskiyar magana ita ce, aiki ne na farkon wanda ya horar da waɗannan zaƙaƙuran jami’ai, da farko sun kasance kamar ba za su iya ba, lallai ka gudanar da gagarumin aiki wanda ka cancanci yabo, hukumar gudanarwa ta NIS tana alfahari da kai bisa jajircewa wajen gudanar da aiki.” In ji CGI Jere.

Ana sa rai waɗannan jami’ai mata su taimaka wa ƙarfafa tsaron iyakokin da za a tura su kamar yadda NIS ta ƙudurta bisa jagorancin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

Next Post

Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

Related

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

10 minutes ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

2 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

3 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

7 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

8 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

17 hours ago
Next Post
Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

LABARAI MASU NASABA

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.