An fara zaman makokin kwanaki uku a ƙasar Austria bayan wani tsohon ɗalibi ya dawo makarantarsa, ya buɗe wuta, inda ya kashe mutane tara.
Ya kashe ɗaliban kafin daga bisani jami’an tsaro su harbe shi har lahira.
- Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD
- Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu
Lamarin ya faru a birnin Graz da ke kudu maso gabashin ƙasar.
Shugaban gwamnati, Christian Stocker, ya bayyana ranar da lamarin ya faru a matsayin rana mai matuƙar baƙin ciki ga ƙasar Austria.
Ya ce harin bai kamata ya faru ba a ƙasa kamar Austria ba.
Bayanai sun nuna cewa, harin na faruwa, aka sanar da jami’an tsaro.
Sun isa cikin gaggawa da motocinsu da jirgin sama mai saukar ungulu.
Amma maharin ya ƙi miƙa wuya, hakan ya sa aka bindige shi.
Daga cikin waɗanda suka mutu, mata shida ne, maza uku, sannan wasu da dama sun jikkata sakamakon harbin bindiga.
Hukumomi sun ce har yanzu suna ci gaba da bincike don samo ƙarin bayani game da wannan mummunan al’amari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp