ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Shugaban Tarayyar Sobiet Mikhail Gorbacheb Ya Rasu

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Sobiet

Shugaban Tarayyar Sobiet na karshe Mikhail Gorbacheb, ya mutu yana da shekara 91. Mista Gorbacheb, wanda ya karbi ragamar mulki a 1985, ya yi fice wajen bude kofofin tsohuwar Tarrayar Sobiet da kuma kusancinsa da kasashen Yamma, amma ya kasa hana kasarsa rugujewa a 1991.

‘Yan kasar Rasha da dama sun dora alhakin rugujewar Tarrayar Sobiet a kan manufofinsa na kawo sauyi. Jami’an asibitin da ya mutu sun ce ya yi fama da doguwar rashin lafiya. Shugaban kasar Rasha, Bladimir Putin, ya bayyana alhininsa game da mutuwar Mista Gorbacheb, kamar yadda mai magana da yawunsa Dmitry Peskob ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Rasha Interfad a cewar Reuters.

  • Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma
  • …Dalla-dallar Yadda Aka Kashe Kudin Tallafin Mai

Mista Gorbacheb ya zama babban sakataren jam’iyyar gurguzu ta tsohuwar Tarayyar Sobiet da kuma shugaban kasa yana da shekara 54.

ADVERTISEMENT

A wancan lokaci shi ne mamba mafi karancin shekaru a majalisar da ke mulki da aka fi sani da Politburo, kuma ana kallonsa a matsayin matashi mai kwarjini, bayan shekarun da aka shafe ana samun shugabannin da suka tsufa.

Manufarsa ta bai wa al’ummar kasar damar bayyana ra’ayoyinsu ciki har da sukar gwamnati wanda wani abu ne mai wuya a baya. Sai dai ta sa yankuna da dama sun fara neman ‘yancin kai, wanda a karshe ya kai ga rugujewarta.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A matakin kasa da kasa ya cimma yarjejeniyar takaita amfani da makamai tsakanin kasarsa da Amurka, kuma ya ki shiga tsakani a lokacin da kasashen gabashin Turai suka yi wa shugabanninsu masu ra’ayin gurguzu bore.

Kasashen yammacin duniya na kallonsa a matsayin wanda ya jagoranci yadda za a kawo karshen yakin cacar[1]baka.

An ba shi lambar yabo ta zaman lafiya ta Nobel a shekara ta 1990, saboda rawar da ya taka wajen kawo sauye[1]sauye a dangantakar da ke tsakanin kasashen Gabashi da na Yamma.

Sai dai a sabuwar Rashar da ta bayyana bayan 1991, ya nesanta kansa daga harkar siyasa inda ya mayar da hankali a kan ilimi da ayyukan jin kai.

Ya yi yunkurin komawa fagen siyasa a 1996, amma kashi 0.5 na kur’iun da aka kada ne ya samu a zaben shugaban kasa. A shekarun baya-bayan nan ya rika fama da rashin lafiya kuma an rika jinyarsa a asibiti.

Kamfanin dillancin labarai na Tass ya ce za a binne shi a makabartar Nobodebichy da ke birnin Moscow, inda a nan ne ake binne fitattun ‘yan kasar, kusa da matarsa Raisa wadda ta mutu a 1999.

Sobiet
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Kasashe Da Dama Na Sa Ran Habaka Kasuwannin Cinikayyar Hidimomin Kasar Sin Ta Hanyar Halartar Bikin CIFTIS

Kasashe Da Dama Na Sa Ran Habaka Kasuwannin Cinikayyar Hidimomin Kasar Sin Ta Hanyar Halartar Bikin CIFTIS

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.