ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashe Da Dama Na Sa Ran Habaka Kasuwannin Cinikayyar Hidimomin Kasar Sin Ta Hanyar Halartar Bikin CIFTIS

by CMG Hausa
4 years ago
CIFTIS

A halin yanzu, ana gudanar da bikin cinikayyar hidimomi na kasa da kasa na shekarar 2022 wato CIFTIS a takaice a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

A bana, akwai kasashe da kungiyoyin kasa da kasa guda 71 da suka kafa shagunan nune-nune ko shirya taruka a wajen bikin na wannan karo.

  • Bikin CIFTIS Zai Samar Da Damar Raya Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Bangarori Daban Daban

Ciki har da kasashe guda 10 da suka hada da kasar Switzerland, da Burundi, da haddadiyar daular Larabawa da sauransu, wadanda a karo na farko, suka kafa shagunan nune-nune a yayin bikin CIFTIS da sunayen kasashensu.

ADVERTISEMENT

Jami’in sashen kula da harkokin tattalin arziki na ofishin jakadancin haddadiyar daular Larabawa dake nan kasar Sin, Saeed Alghfeli ya bayyana cewa, bikin CIFTIS ya kasance daya daga cikin muhimman dandaloli guda uku, dake bayyana yadda kasar Sin take bude kofarta ga ketare.

Kuma a yayin bikin na wannan karo, kasarsa na fatan gabatar da karin bayanai game da tattalin arzikinta ga masu zuba jari na kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

A yayin wannan biki, a karo na farko, Italiya ta kafa wani shagon nune-nune da sunanta. Wakilin ofishin birnin Beijing na kwamitin cinikin waje na kasar Italiya Gianpaolo Bruno ya bayyana fatan samun karin abokan hadin gwiwa a yayin wannan biki.

Kasar Cyprus tana yankin iyaka dake tsakanin nahiyar Turai, da ta Asiya, da ma ta Afirka. Minista mai kula da harkokin tattalin arziki da ciniki na ofishin jakadancin kasar Cyprus dake kasar Sin Petrou Petros ya ce, a karo na farko, kasarsa ta kafa shagon nune-nune a yayin bikin CIFTIS da sunanta, domin tana fatan gabatar wa karin abokai na kasar Sin, sana’ar hidimomi da ke akwai a kasar Cyprus.

Cikin shekaru 10 da suka gabata, darajar hidimomin da kasar Sin ta shigo daga ketare ta zarce dallar Amurka triliyan 4.

A matsayin wani muhimmin bikin baje koli na kasa, bikin CIFTIS ya samar da damamaki masu dimbin yawa daga dukkan fannoni ga kamfanonin kasashen duniya, domin su shiga manyan kasuwannin kasar Sin. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

CIFTIS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Binciki Musabbabin Rushewar Benen Titin Beirut -Ganduje

Gwamnatin Kano Za Ta Binciki Musabbabin Rushewar Benen Titin Beirut -Ganduje

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.