• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

by Sulaiman
2 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan Adam halitta ce mai saurin mantuwa. Duk da haka, akwai wasu abubuwa da ya kamata a tuna da su.

 

Abokai, ko kun san cewa, sama da shekaru 80 da suka gabata, ‘yan Najeriya da Sinawa sun taba yaki da sojojin Japan a Burma, inda suka bayar da gagarumar gudunmawa wajen cin nasarar yakin da aka yi da ‘yan mulkin danniya, wato ‘yan Fascist a duniya?

  • APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici
  • Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

A farkon shekarar 1944, Birtaniya ta tura wasu sojoji da aka dauka daga Najeriya, da Gold Coast (Ghana a yanzu) da sauran wurare, zuwa yankin kan iyakar Indiya da Burma. Daga lokacin har zuwa shekarar 1945, sojoji ‘yan Afirka sun yi ta kokarin yaki da sojojin Japan a Burma. Inda bajintar da wadannan sojojin Afirka suka nuna a yaki ta bar ma makiya mamaki matuka.

 

Labarai Masu Nasaba

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

A lokacin kasar Sin ba ta tsaya kan tinkarar mahara Japanawa a ciki gidanta kadai ba, har ma bisa bukatar Birtaniyya, ta tura sojoji zuwa kasar Burma don tallafawa yakin da ake yi da sojojin Japan a can. Daga watan Oktoba na 1943 zuwa na Maris na 1945, sojojin kasar Sin sun hallaka sojojin Japan sama da 49,000, tare da kwato garuruwa da Japanawa suka mamaye sama da 50 a arewacin Burma. Sojojin kasar Sin sun kuma yi asara sosai, inda yawan mutanensu da suka rasa rai ko kuma suka ji rauni ya kai sama da 60,000.

 

Gudunmawar da magabata suka bayar, abu ne da ya kamata a tuna da shi. Mun san daga baya, tsoffin sojojin Afirka a yakin duniya na biyu sun taka muhimmiyar rawa a gwagwarmayar neman ‘yancin kai na kasashen Afirka, yayin da Sin ma ta tabbatar da matsayinta a idanun mutanen duniya, ta hanyar bayar da gagarumar gudummawa wajen yaki da ‘yan Fascist a duniya.

 

Kuma domin tunawa da tarihi ne, a jiya (15 ga watan Agusta, wato ranar cikar shekaru 80 da kasar Japan ta mika wuya ba tare da wani sharadi ba ga kawancen yaki da ‘yan Fascist), na ziyarci gidan tarihi na tunawa da yakin kin harin Japan da jama’ar kasar Sin suka yi, da ke birnin Beijing na Sin, domin maimaita tarihin yadda jama’ar kasar Sin suka yi tsayin daka wajen adawa da zaluncin mahara Japanawa. Ta hanyar kallon abubuwan da aka adana, da hotuna, da bidiyo, da rubutaccen bayanin da aka nuna, na sake gane wa idona irin ta’asar da mahara Japanawa suka aikata: kisan kiyashin da aka yi wa mutane kimanin 300,000 a Nanjing, babban birnin kasar Sin a lokacin; da yadda rundunar 731 ta kasar Japan ta gudanar da gwaje-gwajen kai tsaye kan jama’ar kasar Sin masu rai, don bincike da kera makaman kare dangi masu guba; da yadda sojojin Japan suka yi kokarin tabbatar da ganin a kona dukkan gidaje, da kashe dukkan mutane, da kuma kwace dukkan dukiyoyi, a dimbin kauyuka marasa adadi na kasar Sin. A sa’i daya kuma, na ji irin ruhin da jama’ar kasar Sin suke da shi na hakuri da jure wahalhalu, da yadda suke matukar kokari wajen tabbatar da samun nasara a yakin kin harin Japan. A yakin da aka kwashe shekaru 14 ana yinsa, kasar Sin ta samu asarar sojoji da fararen hula (mutuwa ko jin rauni) sama da miliyan 35, wato adadin kusan kashi daya bisa uku na jimillar wadanda suka mutu ko suka ji rauni a yakin duniya na biyu a fadin duniya.

 

Har ila yau, a zamanin da muke ciki, tunawa da tarihi yana da ma’anar musamman:

Ta hanyar tunawa da tarihi, muna dakile yunkurin mutanen da suke kokarin boye gaskiya, inda za mu tunatar da su cewa kisan kiyashi na Nanjing, da ta’asar da rundunar 731 ta aikata, abubuwa ne na gaske da suka taba faruwa, wadanda ba za a iya goge su daga cikin tarihi ba, kuma kasar Japan ba za ta iya tserewa alhakin laifukan cin zarafin bil’adama ba; kana za mu bayyana karara cewa, komawar yankin Taiwan zuwa cikin harabar kasar Sin yana daga cikin sakamakon da aka samu a yakin kin ‘yan Fascist a duniya, wadda ba za a iya gyara ta ba.

Haka zalika, tunawa da tarihi yana ba mu damar gadon ruhin hadin kai da gwagwarmaya. Jama’a daga ko’ina cikin duniya, ciki har da Afirka da Sin, sun taba yin hadin gwiwa karkashin tutar adalci, inda suka yi fafutuka kafada da kafada, don tabbatar da makoma mai haske ta bil’adama. Wannan ruhin yanzu an mai da shi ya zama niyyar gina “al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya,” wadda ta sanya mu yin aiki tare don samun zaman lafiya a duniya, da ci gaban bai daya a tsakanin dukkanin kasashe.

 

Tunawa da tabbatar da tarihi za su karfafa imaninmu kan cewar, wadanda ke neman yin kashin dankali a duniya ba za su samu biyan bukata ba, kuma nasara ta karshe za ta kasance ta mutane, da kasashe masu ra’ayin daukaka zaman lafiya da tabbatar da yanayin adalci a duniya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici

Next Post

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

Related

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

5 days ago
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

6 days ago
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

1 week ago
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

1 week ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

2 weeks ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

2 weeks ago
Next Post
Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.