• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

by Sulaiman
9 months ago
in Tattaunawa
0
Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tattaunawar Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, da gidan talabijin na Aljazeerah a ranar Asabar, 3 ga Agusta, 2024. Ga yadda Tattaunawar ta kasance:

 

Mungode da kasancewar ka tare da mu a yau a cikin shirin Inside Story. Minista Idris, ƙungiyar Amnesty International ta ce, jami’an tsaro sun kashe masu zanga-zangar lumana 13 a faɗin ƙasar nan kuma ta yi Allah-wadai da hakan. Me gwamnati za ta ce a kan hakan?

To, da farko dai gwamnati ta nanata irin wannan tsokaci na cewa, da zarar an bar irin wannan zanga-zangar ta faru, to akwai yiwuwar ta zama tarzoma ko hargitsi. Yawancin mutanen da suka fita kan tituna a safiyar ranar Alhamis sun kasance cikin kwanciyar hankali da sanyin safiyar. Don haka ‘yansanda sun raka waɗannan masu zanga-zangar, tare da tabbatar da cewa, komai ya daidaita, kafin mutane su mayar da lamarin zuwa wata tarzoma, kuma hakan ba abu ne da za a amince da shi ba ne.

Rahoton na Amnesty International bai nuna cewa ‘yansanda ba kawai sun yi ta harbin mutane ba. Masu zanga-zangar sun bi kan tituna inda suka fara ƙona ababen hawa tare da wawushe shaguna. Ba zai yiwu ba jami’an tsaro su zauna su ƙyale waɗannan abubuwa su faru. Don haka, a zahiri zanga-zangar lumana ce ta rikide zuwa hargitsi. Gwamnati da jami’an tsaro suna tabbatar da cewa, komai ya daidaita.

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

Amma ku tuna cewa kafin wannan lokacin, a koda yaushe muna gargaɗin cewa, masu zanga-zangar su yi watsi da wannan shiri, domin tarihinmu ya nuna cewa, da zarar an fara fita kan tituna, akwai yiwuwar gungun masu aikata laifuka ko masu aikata miyagun laifuka su bi kan tituna su yi tashin hankali. Mun ga hakan ya faru a kai-a kai a ƙasar nan, shi ya sa muka nace a matsayinmu na gwamnati cewa, ba a buƙatar zanga-zanga.

Kafin wannan rana, za ku tuna cewa sun bayar da kwanaki ko makwanni da yawa kafin wannan ranar ta zo. Muna ta aika saƙon mu: don Allah a watsar da shi, gwamnati na sauraronku. Tuni dai wannan gwamnati ta fara aiwatar da gyare-gyare domin ganin cewa an riga an magance buƙatun da waɗannan masu zanga-zangar suka gabatar. Tattalin arziki ya kasance cikin mummunan yanayi kafin wannan gwamnatin. Ku tuna cewa, kun san babu wani tanadi da aka yi na kasafin kuɗi a watan Yuni na shekarar da ta gabata, lokacin da gwamnati ta zo a ranar 29 ga watan Mayun 2023, ba a yi kasafin kuɗin ƙarin tallafi ba.

Tun da kana maganar kasafin kuɗi, masu sukar batun cire tallafin man fetur, sun ce, cire shi a lokacin da Shugaba Tinubu ya yi, hakan ya yi wuri da yawa! Sun ce abin ya yi matuƙar rikita tsarin. Me za ka ce ga ‘yan Nijeriya da ke kokawa da matsalar tattalin arziki da ba a taɓa ganin irin sa ba?

 

Mun san cewa za a samu waɗannan wahalhalu kuma za a fuskanci ƙalubale. Ina nufin, halin da tattalin arzikin Nijeriya ke ciki ya yi muni matuƙa. Ba wai tattalin arzikin ƙasar ya taɓarɓare ba ne saboda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya hau mulki. Bayanan suna nan don kowa ya gani, muna cin bashi ne don ci gaba da ɗaukar nauyin wannan tallafin. Don haka, Shugaban Ƙasa ya ji cewa wannan bai zama dole ba. Ba za mu iya ci gaba da rayuwar ƙarya ba. Ya zama dole Nijeriya ta koma ta sake fasalin yanayin tattalin arzikinta, ta magance matsaloli, kuma wasu daga cikin waɗannan matsalolin na iya zama masu zafi sosai. Kuma wannan shi ne dalilin da ya sa gwamnati ta zo da matakai da yawa don rage tasirin. Mun san cewa akwai ƙalubale kuma gwamnati ba ta ce ba ta san hakan ba.

Haka kuma an fitar da wasu batutuwa da dama don tabbatar da cewa duk halin da ake ciki ‘yan Nijeriya za su samu sauƙi a matsakaici da kuma dogon zango. Amma a yanzu, kowa ya jajirce domin tattalin arzikin ƙasar ya taɓarɓare tsawon shekarun da suka gabata, shekaru da yawa na rashin kula. An yi tsare-tsare waɗanda ba don gyara tattalin arziki ba ne. Don haka yana da muhimmanci kuma ya zama wajibi gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta tabbatar an mayar da waɗannan abubuwa.

Menene matakin damuwa a yanzu a cikin gwamnati cewa wannan zanga-zangar za ta haɓaƙa kuma shin Shugaban Ƙasa zai sallama nan gaba?

To, gwamnati za ta ci gaba da yin duk abin da zai yiwu don tabbatar da cewa ’yan ƙasa sun samu daidai. A ko da yaushe muna cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu mai sauraro ce, ba a taɓa yin irin ta ba, sau da yawa idan ana tsare-tsare, kuma ‘yan Nijeriya ba su ji daɗin hakan ba, ko da yaushe gwamnati tana dawowa ta duba waɗannan tsare-tsaren ta yi gyara. Gwamnati tana nan don kare rayuka da dukiyoyi don tabbatar da cewa an yi gyare-gyaren tattalin arziki.

Batun ma’aikata misali ne mai kyau, inda a watan Oktoban shekarar da ta gabata aka samu kyautar albashi da gwamnati ta bayar ta naira 25,000 lokacin da Ƙungiyar Ƙwadago ta zo ta ce naira 25,000 ta yi kaɗan. Muka yi muhawara da su, kuma a ƙarshe an ba su ƙarin naira 10,000. Dubi kuma abin da ya faru a cikin kwamitin mutum uku da aka kafa don duba sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa, ya zo da kuɗi kusan naira 62,000, Shugaban Ƙasa ya nemi shawara sosai, kuma a ƙarshe an samu ƙarin naira 8,000 ya zama naira 70,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa, Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya tana nan, ba abin da suke so ba ne, amma tabbas su ma sun karɓe shi, muka gama da wannan.

Da farko dai masu wannan zanga-zangar ba su bayyana kan su ba, yawancin abin da muke gani a intanet ne, a shafukan sada zumunta, suna cewa mutane za su yi zanga-zanga, kuma mun damu matuƙa, domin idan ba ku da shugabancin da ya dace, idan ba ku da shugabanni da tun farko za a iya magana da su, shi ya sa ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro suka buƙaci waɗannan shugabannin da su fito, kuma ba shakka wasu daga cikin su sun fito a ƙarshe, amma ba a san galibin shugabannin masu zanga-zangar ba, kuma wannan ita ce damuwar da muke da ita.

Zanga-zanga wani ɓangare ne na dimokiraɗiyya, muna gudanar da tsarin dimokiraɗiyya. Shugaban Ƙasa ya yi imanin cewa ‘yan ƙasa na da ‘yancin yin zanga-zanga a duk lokacin da suka ji cewa tsare-tsare ba su tafiya daidai, amma abin tsoro a ko da yaushe shi ne cewa wannan zanga-zangar na iya komawa tarzoma kuma abin da ya faru kenan, zanga-zangar ta koma tarzoma a sassa da dama na ƙasar nan, kuma wannan ita ce damuwar da muke da ita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amosanin jiniGwamnatin TinubuTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zanga-zanga: Hukumar DSS Ta Kama Jagoran #EndbadGovernance A Abuja

Next Post

Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu

Related

Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya
Tattaunawa

Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya

7 months ago
Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u
Tattaunawa

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

7 months ago
Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka
Tattaunawa

Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka

9 months ago
Rashin Amfani Da Ilimin Taurari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki – Sheikh Muhajjadina
Tattaunawa

Rashin Amfani Da Ilimin Taurari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki – Sheikh Muhajjadina

9 months ago
Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa
Tattaunawa

Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

10 months ago
Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina
Tattaunawa

Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina

10 months ago
Next Post
Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu

Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.