• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uba Sani Ya Rantsar Da Manyan Jami’an Gwamnati Biyu A Jihar Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Uba Sani Ya Rantsar Da Manyan Jami’an Gwamnati Biyu A Jihar Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bukaci sabon babban sakatare na musamman (PPS) da aka rantsar, Farfesa Bello Ayuba, da kuma mai kula da birnin Kaduna (KCT), Samuel Aruwan, da su nuna kwarewarsu akan nadin da aka yi musu don ci gaban jihar Kaduna.

Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ne ya bukace su da hakan a lokacin da yake rantsar da manyan jami’an gwamnatin biyu a dakin taro na gidan gwamnati (Sir Kashim Ibrahim House) a ranar Litinin.

  • Da Zaman Lafiya Ake Samun Ci Gaba – Sanata Uba Sani 

Ya kuma bukace su da su yi amfani da sabbin mukamansu wajen fifita bukatun jama’a akan na su, yana mai cewa, wadanda aka nadan sun kasance kwararrun ‘yan jarida ne kafin su kai ga matsayin da suke a yanzu.

Ya ce, “Farfesa Bello Ayuba ya taba zama Shugaban Ofishin Jarida ta ‘Today’s newspaper’ ta Bauchi, Shugaban Kungiyar Marubuta Wasanni ta Nijeriya (SWAN) da sauransu, kafin ya koma bangaren karantarwa a jami’a inda ya bayyana kansa a matsayin kwararre a fannin ilimi da kuma gudanarwa.

“Shi kuma mai kula da babban birnin Kaduna, Samuel Aruwan ya yi aiki da jaridar ‘Daily Independent, LEADERSHIP da Blueprint’ kafin ya shiga aikin gwamnati inda kuma ya rike mukamai daban-daban, ciki har da kwamishinan ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida.”

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

Da yake zantawa da manema labarai bayan rantsar da shi, Farfesa Bello Ayuba, ya bayyana kudirinsa da himmarsa na yin aiki tukuru domin ci gaban jihar, inda ya ce, ashirye yake da ya taimaka wa shugabanmu, gwamna Uba Sani don samun nasara akan karagar jagorantar jihar Kaduna.

Hakazalika, Samuel Aruwan, shugaban hukumar kula da birnin Kaduna (KCT), ya bayyana kudurinsa na ganin birnin Kaduna ya zama birni mai kyau da zaman rayuwa wanda zai yi gogayya da sauran biranen duniya.

Gwamna Uba Sani ya sake nada Samuel Aruwan kwamishinan kula da ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida na wucin gadi kafin a nada sabon kwamishinan ma’aikatar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin bikin rantsar da jami’an gwamnatin biyu a dakin taro na gidan gwamnati da ke Kaduna a ranar Litinin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Sin Ya Gana Da Wakilin Amurka Kan Sauyin Yanayi

Next Post

Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa

Related

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

42 minutes ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

2 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

3 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

5 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

5 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

8 hours ago
Next Post
Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa

Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.