• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

UEFA Champions League: Yaushe Za A Sauya Fasalin Gasar?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
UEFA

A cikin wannan satin ne aka dawo ci gaba da buga wasannin gasar cin kofin zakarun Turai na Champions League na kakar wasa ta shekarar 2023 zuwa 2024 da za’a buga wasan karshe a filin wasa na Wembley dake Landan ta Ingila.

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City za ta yi kokarin kare kofin Champions League a makon nan, inda ta fara wasan rukuni da kungiyar Crbena Zbezda ranar Talata.

  • UEFA Champions League: Real Madrid Ta Sha Da Kyar A Hannun Union Berlin

Manchester City wadda mai koyarwa Pep Guardiola ke jan ragama za ta wakilci Ingila tare da Arsenal da Manchester United da kuma Newcastle, wadda rabonta da gasar ya kai sama da shekara 20.

Kungiyar Newcastle United tana rukuni mai sarkakiya na shida, wanda ya hadar da kungiyoyin Paris St-Germain da AC Milan da kuma Borussia Dortmund, rukunin da ake kira “rukunin mutuwa”.

Manchester City na rukuni na uku da ake cewa ba za ta fuskanci kalubale ba, da ya kunshi RB Leipzig da Red Star Belgrade da kuma Young Boys sai Celtic, wadda ake ganin za ta iya zuwa zagayen gaba, tana rukunin da ya kunshi Feyenoord da Atletico Madrid da kuma Lazio.

LABARAI MASU NASABA

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Kungiyar da take fama da kalubale, wato Manchester United ta kece-raini a rukunin farko da ya kunshi Bayern Munich da FC Copenhagen ta kasar Denmark da kuma Galatasaray.

Arsenal tana rukunin da ya hadar da kungiyar da ta lashe gasar Europa League a kakar da ta wuce, wato kungiyar kwallon kafa ta Sebilla da kuma PSB Eindhoben da Lens ta kasar Faransa.

Sai dai a wannan karon tun bayan da Cristiano Ronaldo da Lionel Messi suka nuna kansu a Turai da taka rawar gani a shekaru da yawa, sai gashi kakar bana ba su a Champions League.

Ronaldo shi ne na farko da ya koma kasar Saudi Arabia – yana kungiyar Al Nassr – shi kuwa Messi yana Amurka a Inter Miami, sai kuma fitattun ‘yan wasan da babu su a Champions League a kakar nan sun hada da dan kwallon Brazil, Neymar da dan kasar Faransa, Karim Benzema, wanda ya koma Al-Ittihad, shi kuwa Neymar na Al Hilal dukkansu a Saudi Arabia.

Ranakun Da Za A Buga Wasannin Champions League:
Ranar wasannin farko: 19 zuwa 20 ga watan Satumba. Ranar wasa na biyu: 3 zuwa 4 ga watan Oktoba. Ranar wasa na uku: 24 zuwa 25 ga watan Oktoba. Ranar wasa na hudu: 7 zuwa 8 ga watan Nuwamba. Ranar wasa na biyar: 28 zuwa 29 ga watan Nuwamba. Ranar wasa na shida: 12 zuwa 13 ga watan Disamba.

Wasannin zagayen ‘yan 16: 13 zuwa 14 da 20 zuwa 21 ga Fabraiirun shekara ta 2024 da kuma 5 zuwa 6 da 12 zuwa 13 ga watan Maris, sai wasannin dab da kusa da na karshe: 9 zuwa 10 da 16 zuwa 17 April.
A dai gasar ta bana ta kofin zakarun Turai da aka fara bugawa a wannan satin, za’a buga wasan dab da karshe a ranar 30 ga Afirilu da 1 ga watan Mayu da 7 zuwa 8 ga watan Mayu sai kuma wasan karshe da za’a buga ranar 1 ga watan Yuni.

An yi hasashen cewar Manchester City ce za ta kara lashe kofin Champions League ba wai Real Madrid ko Bayern Munich ba, in ji wata kididdiga daga Gracenote Euro Club Inded, wadda ke auna kokarin kungiyoyi a wasanninsu.

Manchester City tana da kaso 37 cikin 100 a damar lashe kofin, Real tana da kaso 13 cikin 100 da kuma Bayern mai kaso 11 cikin 100, haka kuma akwai damar wata sabuwar kungiyar ta lashe kofin da kaso 19 cikin 100.
Sannan Manchester City da Real Madrid da Bayern Munchen da kuma Barcelona, dukkansu suna da kaso 90 cikin 100 ta kai wa zagaye na biyu a wasannin gasar ta bana. Sannan wannan ce kakar karshe daga ita za a sauya fasalin wasannin kungiyoyi 32 ne aka raba su rukuni takaws dauke da hur-hudu kowanne, biyu da suka ja ragamar rukuni su kai zagaye na biyu zuwa kwata fainals da dab da karshe da karawar karshe, amma kuma daga kakar wasa ta 2024 zuwa 2025 kungiyoyi 36 ne za su kece raini a tsakaninsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
Wasanni

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray
Wasanni

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
Wasanni

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Next Post
Ten hag

Zan Shawo Kan Matsalar Da Ta Addabe Mu, In Ji Ten Hag

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.