• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

by Bello Hamza
2 months ago
in Labarai
0
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani mataki na sauƙaƙa samun damar yin biza na Birtaniya ga matafiya daga Arewacin Nijeriya, kamfanin VFS Global tare da haɗin gwiwar Hukumar Biza da Shige da Fice ta Birtaniya (UKVI) sun kaddamar da sabuwar Cibiyar Aikace-aikacen biza ta Musamman a Kano.

An buɗe cibiyar ne a Bristol Palace Hotel, lamba 54–56 titin Guda Abdullahi, inda za ta bai wa mazauna Kano da sauran yankunan Arewa damar gabatar da buƙatun biza da yin rijista cikin sauƙi, musamman kafin lokacin tafiye-tafiyen bazara da ke tunkarowa.

  • Kasar Sin Ta Ba Baki Masu Yawon Bude Ido Dake Cikin Jiragen Ruwa Na Nishadi Izinin Shiga Kasar Ba Tare Da Visa Ba 
  • Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Hajiya Gill Lever, wadda ke matsayin Chargée d’Affaires a ofishin jakadancin Birtaniya da ke Abuja, ta bayyana jin daɗinta game da faɗaɗa ayyukan bada biza a Nijeriya.

“Ina farin cikin tabbatar da ci gaba da faɗaɗa ayyukan bada biza na Birtaniya a faɗin Nijeriya, da kaddamar da sabuwar Cibiyar Aikace-aikace ta Musamman ta VFS a Kano,” in ji ta. “Kano da sauran Arewacin Nijeriya na da matuƙar muhimmanci a dangantakar Birtaniya da Nijeriya. Sabuwar cibiyar za ta taimaka wajen sauƙaƙa wa mutane samun ingantaccen sabis na biza a kusa da inda suke.”

Ta kuma bayyana cewa Nijeriya na daga cikin ƙasashen da ke da yawan masu ziyartar Birtaniya daga nahiyar Afirka, inda take cikin ƙasashe huɗu mafi yawan masu nema, kuma tana da kusan kashi 6 cikin 100 na adadin aikace-aikacen biza a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Wannan cibiyar da aka buɗe a Kano ita ce ta uku da VFS Global ta kaddamar a cikin ‘yan watannin baya a Nijeriya, bayan buɗe makamantansu a Enugu da Port Harcourt. Cibiyoyin na ƙara wa waɗanda ke Abuja da Legas (Ikeja da Victoria Island), waɗanda ke aiki tun daga Nuwamba 2024.

Mista Alok Singhal, shugaban yankin hamadar nahiyar Afirka na VFS Global, ya jaddada aniyar kamfanin na kawo sauƙi ga abokan cinikinsu.

“Muna farin ciki da ƙara yawan wuraren da za a iya samun sabis na biza cikin sauƙi ga ‘yan Nijeriya, musamman da buɗe sabuwar cibiyar mu ta Musamman a Kano,” in ji shi. “Yayin da buƙatar tafiya zuwa Birtaniya ke ƙaruwa, burinmu shi ne mu samar da irin ingantaccen sabis, sauƙi da jin daɗi da muke bayarwa a Abuja da Legas a nan Kano.”

Sabuwar cibiyar da ke Kano na bayar da sabis na musamman da suka haɗa da taimako wajen lodin takardu, sanarwa kai-tsaye kan matsayin aikace-aikace, da isar da takardu ta hanyar sakonni. Haka kuma, abokan ciniki za su iya amfani da sabis ɗin “Ajiye Fasfo ɗina Bayan sa hannu”, wanda ke ba su damar ci gaba da amfani da fasfo ɗinsu bayan rijistar, sannan su miƙa shi daga baya idan an yanke hukunci.

Kamfanin VFS Global wanda ke aiki da ‘UK Visas and Immigration’ tun shekarar 2003, ya soma bayar da sabis a ƙasashe 58. A shekarar 2023, an sake ba su kwangilar bayar da sabis a ƙasashe 142, alamar yarda da ƙwarewarsu a fannin.

Ga mazauna Kano da sauran yankunan Arewacin Nijeriya, wannan sabuwar cibiyar na nufin ƙarin sauƙi, jin daɗi da saurin aiki – wanda zai ƙarfafa dangantaka tsakanin Nijeriya da Birtaniya a fannonin kasuwanci, yawon buɗe ido, ilimi da musayar al’adu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BirtaniyaBizakanoVisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Next Post

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Related

Kano
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

2 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

2 hours ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

3 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

3 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 19-09-2025

4 hours ago
Kano
Labarai

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

5 hours ago
Next Post
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

LABARAI MASU NASABA

Kano

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Kano

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.