• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

by Bello Hamza
3 months ago
Kano

A wani mataki na sauƙaƙa samun damar yin biza na Birtaniya ga matafiya daga Arewacin Nijeriya, kamfanin VFS Global tare da haɗin gwiwar Hukumar Biza da Shige da Fice ta Birtaniya (UKVI) sun kaddamar da sabuwar Cibiyar Aikace-aikacen biza ta Musamman a Kano.

An buɗe cibiyar ne a Bristol Palace Hotel, lamba 54–56 titin Guda Abdullahi, inda za ta bai wa mazauna Kano da sauran yankunan Arewa damar gabatar da buƙatun biza da yin rijista cikin sauƙi, musamman kafin lokacin tafiye-tafiyen bazara da ke tunkarowa.

  • Kasar Sin Ta Ba Baki Masu Yawon Bude Ido Dake Cikin Jiragen Ruwa Na Nishadi Izinin Shiga Kasar Ba Tare Da Visa Ba 
  • Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Hajiya Gill Lever, wadda ke matsayin Chargée d’Affaires a ofishin jakadancin Birtaniya da ke Abuja, ta bayyana jin daɗinta game da faɗaɗa ayyukan bada biza a Nijeriya.

“Ina farin cikin tabbatar da ci gaba da faɗaɗa ayyukan bada biza na Birtaniya a faɗin Nijeriya, da kaddamar da sabuwar Cibiyar Aikace-aikace ta Musamman ta VFS a Kano,” in ji ta. “Kano da sauran Arewacin Nijeriya na da matuƙar muhimmanci a dangantakar Birtaniya da Nijeriya. Sabuwar cibiyar za ta taimaka wajen sauƙaƙa wa mutane samun ingantaccen sabis na biza a kusa da inda suke.”

Ta kuma bayyana cewa Nijeriya na daga cikin ƙasashen da ke da yawan masu ziyartar Birtaniya daga nahiyar Afirka, inda take cikin ƙasashe huɗu mafi yawan masu nema, kuma tana da kusan kashi 6 cikin 100 na adadin aikace-aikacen biza a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Wannan cibiyar da aka buɗe a Kano ita ce ta uku da VFS Global ta kaddamar a cikin ‘yan watannin baya a Nijeriya, bayan buɗe makamantansu a Enugu da Port Harcourt. Cibiyoyin na ƙara wa waɗanda ke Abuja da Legas (Ikeja da Victoria Island), waɗanda ke aiki tun daga Nuwamba 2024.

Mista Alok Singhal, shugaban yankin hamadar nahiyar Afirka na VFS Global, ya jaddada aniyar kamfanin na kawo sauƙi ga abokan cinikinsu.

“Muna farin ciki da ƙara yawan wuraren da za a iya samun sabis na biza cikin sauƙi ga ‘yan Nijeriya, musamman da buɗe sabuwar cibiyar mu ta Musamman a Kano,” in ji shi. “Yayin da buƙatar tafiya zuwa Birtaniya ke ƙaruwa, burinmu shi ne mu samar da irin ingantaccen sabis, sauƙi da jin daɗi da muke bayarwa a Abuja da Legas a nan Kano.”

Sabuwar cibiyar da ke Kano na bayar da sabis na musamman da suka haɗa da taimako wajen lodin takardu, sanarwa kai-tsaye kan matsayin aikace-aikace, da isar da takardu ta hanyar sakonni. Haka kuma, abokan ciniki za su iya amfani da sabis ɗin “Ajiye Fasfo ɗina Bayan sa hannu”, wanda ke ba su damar ci gaba da amfani da fasfo ɗinsu bayan rijistar, sannan su miƙa shi daga baya idan an yanke hukunci.

Kamfanin VFS Global wanda ke aiki da ‘UK Visas and Immigration’ tun shekarar 2003, ya soma bayar da sabis a ƙasashe 58. A shekarar 2023, an sake ba su kwangilar bayar da sabis a ƙasashe 142, alamar yarda da ƙwarewarsu a fannin.

Ga mazauna Kano da sauran yankunan Arewacin Nijeriya, wannan sabuwar cibiyar na nufin ƙarin sauƙi, jin daɗi da saurin aiki – wanda zai ƙarfafa dangantaka tsakanin Nijeriya da Birtaniya a fannonin kasuwanci, yawon buɗe ido, ilimi da musayar al’adu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

hisba
Labarai

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya
Labarai

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Next Post
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

LABARAI MASU NASABA

hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025
Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

October 12, 2025
Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 12, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

October 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.