• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wai Kasar Sin Na Yin Matsin Tattalin Arziki? Lallai Mataki Ne Da Amurka Ta Dauka Don Dakile Ta

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wai Kasar Sin Na Yin Matsin Tattalin Arziki? Lallai Mataki Ne Da Amurka Ta Dauka Don Dakile Ta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya ne aka rufe taron kolin kungiyar G7 na tsawon yini uku a birnin Hiroshima na kasar Japan. Sai dai hadaddiyar sanarwar da taron ya fitar ta kara wa batutuwan da suka shafi kasar Sin gishiri, inda mahalarta taron suka yi barazanar daukar matakai na tinkarar abin da suka kira wai “matsin tattalin arziki”, matakin da ya bayyana yadda kasashen yammacin duniya da ke karkashin jagorancin kasar Amurka suke yin amfani da kungiyar G7 wajen yin babakere da ma neman dakile kasar Sin.

A zahiri dai, Amurka ce kasar da ke yin matsin tattalin arziki, duba da yadda ta sha daukar matakai na sanya takunkumi da kayyade fitar ko shigar da kayayyaki da kara sanya harajin kwastan da sauransu, don yi wa sauran kasashe matsin tattalin arziki, baya ga kuma yadda take tilasta yin amfani da dokokinta na cikin gida a kan sauran kasashe, da ma tilasta wasu kasashe katse huldar tattalin arziki da su. Hakika matakan da ta dauka na matsin tattalin arziki ba sa lisaftuwa, wadanda suka lalata tsarin samar da kayayyaki na duniya tare da jawo baraka ga kasuwar duniya.

  • Sharhi: Kasashen Duniya Za Su Gano Amsa In Sun Kwatanta Tarukan Koli Na Xi’an Da Hiroshima

Ko da kawayenta da ke cikin kungiyar G7 ma ba su tsira daga matakanta na matsin tattalin arziki ba. In mun duba tarihi, kamfanin Toshiba na Japan da Siemens na Jamus da kuma Alstom na Faransa, wadanda dukkaninsu kamfanoni ne na kasashe kawayen kasar Amurka, duk sun fuskanci irin matakan da Amurka ta dauka, sakamakon yadda suka zama kalubale gare ta. Saboda a ganin kasar Amurka, moriya ce kawai za ta dore a maimakon zumunta.

Sai dai abin takaici ne yadda su kasashe mambobi kungiyar G7 da Amurka ta yi musu illa, har yanzu suke hada kai da Amurka din suke yi wa wasu illar da suka taba fuskanta.

‘Yan siyasa da kafofin yada labarai na Amurka sun kware wajen jirkita gaskiya bisa tasirinsu na iya magana, kuma zancen nan na wai “matsin tattalin arziki” mataki ne da Amurka ta dauka don takura wa kasar Sin. Sanin kowa ne kasar Sin na nacewa ga bin hanyar samun ci gaba cikin lumana, wadda kuma take tsayawa tsayin daka a kan manufar bude kofa ga juna don cin moriyar juna. A cikin shekaru 10 da suka wuce, gudummawar da ta samar wa bunkasuwar tattalin arzikin duniya ta zarce wadda kasashen G7 suka bayar baki daya.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Hasashen da bankin duniya ya yi ya kuma shaida cewa, ya zuwa shekarar 2030, shawarar “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar za ta fitar da mutanen duniya miliyan 7.6 daga matsanancin talauci. Baya ga haka, manyan ababen more rayuwa da kasar Sin ke ginawa a sassan duniya na taimakawa kasashe daban daban raya tattalin arzikinsu. Da hakan muke iya gano cewa,kasar Sin tana samar da zarafi da ci gaba ga duniya a maimakon kalubale da barazana.

Kasancewarsu kasashe masu sukuni, ya kamata kasashen G7 su kara mai da hankali a kan yadda za su taimaka ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma bunkasuwa a duniya, a maimakon neman lalata zaman lafiya da kwanciyar hankalin duniya da ma dalike ci gaban sauran kasashe.(Lubabatu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban DRC Zai Ziyarci Kasar Sin

Next Post

Yanzu-yanzu: Bayan Shafe Mako Guda A Gidan Yari An Saki Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

7 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

7 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

8 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

10 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

11 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

13 hours ago
Next Post
Yanzu-yanzu: Bayan Shafe Mako Guda A Gidan Yari An Saki Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi

Yanzu-yanzu: Bayan Shafe Mako Guda A Gidan Yari An Saki Dakta Idris Abdul'aziz Dutsen Tanshi

LABARAI MASU NASABA

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.