• Leadership Hausa
Thursday, March 23, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wajibi Ne Amurka Ta Cika Alkawarinta

by CMG Hausa
8 months ago
in Labarai
0
Wajibi Ne Amurka Ta Cika Alkawarinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daren 28 ga wannan wata ne, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya tattauna da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden ta wayar tarho, inda ya yi bayani kan nauyin da ke bisa wuyan kasashen Sin da Amurka, ya kuma yi nuni da cewa, Amurka ta yi kuskuren fahimtar dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da kuma bunkasuwar kasar Sin, sa’an nan ya bayyana matsayin kasar Sin kan batun Taiwan.

A nasa bangaren, Biden ya bayyana fatansa na neman hada kai a tsakanin Amurka da Sin, da daidaita sabani yadda ya kamata, ya kuma yi alkawarin cewa, Amurka ba ta sauya kuma ba za ta sauya manufar “kasar Sin daya tak a duniya” ba, ba kuma ta goyon bayan ‘yancin Taiwan.

  • An Tattauna Tsakanin Shugaba Xi Na Sin Da Biden Na Amurka

Wannan ne karo na 5 da shugabannin Sin da Amurka suka tattauna da juna ta wayar tarho, tun bayan Biden ya zama shugaban Amurka.

Kana kuma, tattaunawar da shugabannin 2 suka yi a wannan karo, tana da matukar muhimmanci a wannan muhimmin lokaci. Yanzu haka yaduwar annobar cutar COVID-19 da rikicin Ukraine sun kawo tsaiko ga batutuwan ci gaba da kuma tsaro.

Yayin da kasashen duniya suke fuskantar sauye-sauye da matsaloli, suna fatan Sin da Amurka za su daidaita sabanin dake tsakaninsu yadda ya kamata, za kuma su ba da jagora wajen kiyaye zaman lafiya da tsaro a duniya da kara azama kan bunkasar duniya.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dokokin Kogi Ta Dakatar Da ‘Yan Majalisa 9 D Wasu Kan Zargin Ta’addanci

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

An lura da cewa, a wannan karo, shugaba Xi ya mai da hankali wajen yin bayani kan matsayin kasar Sin game da batun Taiwan, wanda shi ne mafi muhimmanci da kuma jawo hankali a fannin huldar da ke tsakanin Sin da Amurka.

Baya ga haka, a halin yanzu ana kara fuskantar barazana a mashigin tekun Taiwan sakamakon wutar da Amurka take ta rurawa.

Wajibi ne Amurka ta fahimci cewa, idan ba ta tinkari batun Taiwan yadda ya kamata ba, to, za a yi illata huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, wadda ba a taba ganin irinta ba.

Amurka ta sha yin alwashin martaba manufar “kasar Sin daya tak a duniya”, da rashin goyon bayan ‘yancin Taiwan, to, wajibi ne ta cika alkawarinta. (Tasallah Yuan)

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Next Post

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (3)

Related

Majalisar Dokokin Kogi Ta Dakatar Da ‘Yan Majalisa 9 D Wasu Kan Zargin Ta’addanci
Labarai

Majalisar Dokokin Kogi Ta Dakatar Da ‘Yan Majalisa 9 D Wasu Kan Zargin Ta’addanci

27 mins ago
Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara
Manyan Labarai

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

1 hour ago
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu
Manyan Labarai

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

2 hours ago
NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya
Manyan Labarai

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

4 hours ago
FEC Ta Amince Da Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Wajen Gina Barikin Jami’an NDLEA
Labarai

FEC Ta Amince Da Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Wajen Gina Barikin Jami’an NDLEA

6 hours ago
Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna
Labarai

Mata Magoya Bayan PDP Na Zanga-Zangar Watsi Da Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

7 hours ago
Next Post
Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (3)

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dokokin Kogi Ta Dakatar Da ‘Yan Majalisa 9 D Wasu Kan Zargin Ta’addanci

Majalisar Dokokin Kogi Ta Dakatar Da ‘Yan Majalisa 9 D Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 23, 2023
An Yaba Da Yadda Tawagar Likitocin Kasar Sin Ta Ba Da Hidimar Kiwon Lafiya A Sudan Ta Kudu

An Yaba Da Yadda Tawagar Likitocin Kasar Sin Ta Ba Da Hidimar Kiwon Lafiya A Sudan Ta Kudu

March 23, 2023
Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

March 23, 2023
Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

March 23, 2023
Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

March 23, 2023
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

March 23, 2023
Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

March 23, 2023
Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

March 23, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

March 23, 2023
Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

March 23, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.