ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

by Abubakar Sulaiman
1 hour ago
PDP

Wakilai daga jihohi 19 sun isa Ibadan, babban birnin jihar Oyo, a ranar Juma’a, domin halartar taron ƙasa na jam’iyyar PDP wanda za a gudanar a ranar Asabar 15 ga Nuwamba da Lahadi 16 ga Nuwamba. Jihohin da suka halarta sun haɗa da Adamawa, da Akwa Ibom, da Anambra, da Bauchi, da Bayelsa, da Benue, da Borno, da Cross River, da Delta, da Edo, da Ebonyi, da Enugu, da FCT, da Imo, da Kaduna, da Jigawa, da Kano, da Katsina, da kuma Ekiti.

Taron na zuwa ne yayin da jam’iyyar ke fuskantar rikice-rikice na cikin gida da kuma shari’a a kotu. Kwamitin aiki na ƙasa (NWC), ƙarƙashin jagorancin Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Umar Damagum, ya dakatar da Sakatare na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu; Sakatare mai Shirya taro, Umar Bature; da Lauyan jam’iyyar na ƙasa, Kamaldeen Ajibade, bisa zargin aikata abubuwan da suka saɓawa jam’iyya. Wannan mataki ya biyo bayan hukuncin kotun tarayya wanda ya dakatar da taron na ɗan lokaci saboda rashin bin ƙa’idojin gudanarwa, ciki har da gazawar isar da sanarwar taron ga INEC.

  • Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar
  • Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

Sai dai umarnin Alƙali Akintola ya baiwa jam’iyyar dama ta ci gaba da taron. An kammala shirye-shiryen wajen taron a Filin Wasanni na Lekan Salami, inda aka ƙawata shi da launukan jam’iyyar. Ana sa ran wakilai sama da 3,000 daga jihohin tarayya 36 da FCT, tare da shugabanni, masu ruwa da tsaki, da kuma masu sanya ido daga ƙasashen waje zasu halarci taron.

ADVERTISEMENT

Za a gudanar da zaɓen manyan muƙamai na kasa a wannan taro, ciki har da zaɓen Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Sakatare, da sauran manyan jami’an NWC da mataimakansu. A wajen taron, aiyuka na tafiya a ƙarshe, inda aka ɗora tallace-tallace da hotunan yaƙin neman zabe a wurare masu muhimmanci a ciki da wajen filin wasa.

An yi hasashen wannan taro a matsayin ɗaya daga cikin masu jawo cece-kuce mafi girma a tarihin PDP, musamman ma ganin cewa wani ɓangare na jam’iyyar ya janye daga halarta, wanda hakan ya ƙara tsananta yanayin siyasar zaɓen.

LABARAI MASU NASABA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP
Siyasa

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Next Post
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.