ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Arsenal Ta Kammala Daukar Timber

by Sadiq
3 years ago
Arsenal

Arsenal ta kammala daukar dan wasan baya na kasar Netherlands, Jurrien Timber daga Ajax kan kudi fam miliyan 34.

Farashin Timber zai iya tashi zuwa £38.5m idan aka hada da ‘yan tsarabe-tsarabe kuma dan wasan mai shekaru 22 ya koma Arsenal kan yarjejeniya mai tsawo.

  • Kiwon Lafiya: Yadda Dabi’un Ko-in-kula Ke Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
  • Gwamnan Sakkwato Ya Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tambuwal

Zai kara karfafa tsaron Arsenal bayan dan wasan baya William Saliba ya amince da sabon kwantiragin shekaru hudu.

ADVERTISEMENT

Kocin Arsenal Mikel Arteta, ya ce “Muna matukar farin ciki da Jurrien ya iske mu, shi din hazikin matashin mai tsaron baya ne.”

Jurrien matashin dan wasa ne, amma ya riga ya samu nasarori masu yawa,ya buga babbar gasa ta kasa da kasa fiye da sau daya.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Da kuma kofunan da ya lashe tare da Ajax. Muna fatan za a yi maraba da shigar da Jurrien cikin tawagarmu.

Ya buga wa Netherlands wasanni 15, ciki har da hudu a gasar cin kofin duniya da aka buga a Qatar, inda ya taimakawa tawagar Louis van Gaal ta kai wasan daf da na kusa da karshe.

Timber ya ce ya kasance mai sha’awar Arsenal a koyaushe wanda ya samo asali ne daga kaunar da yan uwansa ke nuna wa kulob din.

Timber ya ce ya kasance magoyin bayan Arsenal kullum, kuma ina son ganin Arsenal tana taka leda, suna da manyan yan wasa, yadda suke taka leda abin na burgeni.

Ina son kallon tsoffin yan wasan kungiyar Robin van Persie, da Thierry Henry Su ne yan wasan da na fi so inji shi.

Timber zai kara karfi ga bayan kungiyar Arsenal wadda ta zo ta biyu ga Manchester City a gasar cin kofin Premier da suka fafata a kakar da ta wuce.

Kuma ta samu gurbin shiga gasar cin kofin zakarun Turai bayan shafe shekaru shida ba tare da sun shiga ba.

Timber ya buga wasanni 47 a dukkan gasannin da ya bugawa Ajax a kakar wasan da ta wuce,kuma ya taimakawa kungiyar Amsterdam ta lashe kofin Eredivisie a 2021 da 2022.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Wane Ne Arda Guler Mai Lakabin ‘Sabon Messi A Real Madrid’?

Wane Ne Arda Guler Mai Lakabin ‘Sabon Messi A Real Madrid’?

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.