• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Ministar Harkokin Wajen Jamus 

by CMG Hausa
3 years ago
Wang yi

Asabar din nan ne, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin JKS Wang Yi ya gana da ministar harkokin wajen kasar Jamus Annalena Baerbock a nan birnin Beijing.

A yayin ganawar, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da martaba manufar harkokin waje mai cin gashin kanta, da tabbatar da bin dabarun bude kofa na samun moriyar juna da cimma nasara tare, da kiyaye ikon MDD da tsarin kasa da kasa da aka kafa bayan yakin duniya na biyu. Wang Yi ya kara bayyana cewa, kasar Sin na son karfafa cudanya da mu’amala da kasar Jamus domin inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata.

  • Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanonin Kasar Cikin Jerin Sunayen Kamfanonin Da Ta Sanya Musu Takunkumi

A nata bangare, Baerbock ta ce, kasancewar kasar Sin mambar dindindin a kwamitin sulhu na MDD, kuma kasar Jamus babbar kasa a nahiyar Turai, yana da matukar muhimmanci ga bangarorin biyu su karfafa tattaunawa da mu’amala. Kuma kasarta na martaba manufar Sin daya tak a duniya.

Baya ga haka, a jiya ne, ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya gudanar da taron tattaunawa kan harkokin diplomasiyya da tsaro karo na shida tsakanin kasar Sin da Jamus tare da takwararsa ta kasar ta Jamus Baerbock a nan birnin Beijing.

Wang yi
Wang Yi

A yayin taron, Qin Gang ya ce, kasashen Sin da Jamus abokan hadin gwiwa ne ba abokan gaba ba, kuma ya kamata sassan biyu su bunkasa dangantakarsu da kansu. Kasar Sin tana son yin mu’amala da kasar Jamus tare da inganta hadin gwiwa a dukkan fannoni.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

A nata bangare, Baerbock ta bayyana cewa, kasar Jamus na ci gaba da raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin cikin ‘yanci, kuma tana fatan dawo da mu’amala da tattaunawa a fannoni daban-daban a tsakanin kasashen biyu cikin sauri. Ban da wannan kuma, bangaren Jamus yana mai da hankali sosai kan kiyaye tsarin samar da kayayyaki, bai amince da “mayar da wani bangare saniyar ware a fannin tattalin arziki” ba, kuma yana tsayawa tsayin dak kan nuna daidaito ga kamfanonin juna. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Next Post
Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.