• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Ministar Harkokin Wajen Jamus 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Ministar Harkokin Wajen Jamus 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asabar din nan ne, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin JKS Wang Yi ya gana da ministar harkokin wajen kasar Jamus Annalena Baerbock a nan birnin Beijing.

A yayin ganawar, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da martaba manufar harkokin waje mai cin gashin kanta, da tabbatar da bin dabarun bude kofa na samun moriyar juna da cimma nasara tare, da kiyaye ikon MDD da tsarin kasa da kasa da aka kafa bayan yakin duniya na biyu. Wang Yi ya kara bayyana cewa, kasar Sin na son karfafa cudanya da mu’amala da kasar Jamus domin inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata.

  • Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanonin Kasar Cikin Jerin Sunayen Kamfanonin Da Ta Sanya Musu Takunkumi

A nata bangare, Baerbock ta ce, kasancewar kasar Sin mambar dindindin a kwamitin sulhu na MDD, kuma kasar Jamus babbar kasa a nahiyar Turai, yana da matukar muhimmanci ga bangarorin biyu su karfafa tattaunawa da mu’amala. Kuma kasarta na martaba manufar Sin daya tak a duniya.

Baya ga haka, a jiya ne, ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya gudanar da taron tattaunawa kan harkokin diplomasiyya da tsaro karo na shida tsakanin kasar Sin da Jamus tare da takwararsa ta kasar ta Jamus Baerbock a nan birnin Beijing.

Wang yi
Wang Yi

A yayin taron, Qin Gang ya ce, kasashen Sin da Jamus abokan hadin gwiwa ne ba abokan gaba ba, kuma ya kamata sassan biyu su bunkasa dangantakarsu da kansu. Kasar Sin tana son yin mu’amala da kasar Jamus tare da inganta hadin gwiwa a dukkan fannoni.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

A nata bangare, Baerbock ta bayyana cewa, kasar Jamus na ci gaba da raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin cikin ‘yanci, kuma tana fatan dawo da mu’amala da tattaunawa a fannoni daban-daban a tsakanin kasashen biyu cikin sauri. Ban da wannan kuma, bangaren Jamus yana mai da hankali sosai kan kiyaye tsarin samar da kayayyaki, bai amince da “mayar da wani bangare saniyar ware a fannin tattalin arziki” ba, kuma yana tsayawa tsayin dak kan nuna daidaito ga kamfanonin juna. (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsakanin Samari Da ‘Yan Mata, Wa Ya Kamata Ya Ba Wani ‘Ramadan Basket’

Next Post

Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

Related

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

18 minutes ago
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

1 hour ago
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

2 hours ago
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

3 hours ago
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

22 hours ago
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

23 hours ago
Next Post
Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Wang yi

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Kwanciyar Aure

Yadda Hadarin Mutuwa Ke Karuwa Yayin Ko Bayan Saduwa Da Iyali

July 26, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

July 26, 2025
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.