• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Ministar Harkokin Wajen Jamus 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Ministar Harkokin Wajen Jamus 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asabar din nan ne, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin JKS Wang Yi ya gana da ministar harkokin wajen kasar Jamus Annalena Baerbock a nan birnin Beijing.

A yayin ganawar, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da martaba manufar harkokin waje mai cin gashin kanta, da tabbatar da bin dabarun bude kofa na samun moriyar juna da cimma nasara tare, da kiyaye ikon MDD da tsarin kasa da kasa da aka kafa bayan yakin duniya na biyu. Wang Yi ya kara bayyana cewa, kasar Sin na son karfafa cudanya da mu’amala da kasar Jamus domin inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata.

  • Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanonin Kasar Cikin Jerin Sunayen Kamfanonin Da Ta Sanya Musu Takunkumi

A nata bangare, Baerbock ta ce, kasancewar kasar Sin mambar dindindin a kwamitin sulhu na MDD, kuma kasar Jamus babbar kasa a nahiyar Turai, yana da matukar muhimmanci ga bangarorin biyu su karfafa tattaunawa da mu’amala. Kuma kasarta na martaba manufar Sin daya tak a duniya.

Baya ga haka, a jiya ne, ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya gudanar da taron tattaunawa kan harkokin diplomasiyya da tsaro karo na shida tsakanin kasar Sin da Jamus tare da takwararsa ta kasar ta Jamus Baerbock a nan birnin Beijing.

Wang yi
Wang Yi

A yayin taron, Qin Gang ya ce, kasashen Sin da Jamus abokan hadin gwiwa ne ba abokan gaba ba, kuma ya kamata sassan biyu su bunkasa dangantakarsu da kansu. Kasar Sin tana son yin mu’amala da kasar Jamus tare da inganta hadin gwiwa a dukkan fannoni.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A nata bangare, Baerbock ta bayyana cewa, kasar Jamus na ci gaba da raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin cikin ‘yanci, kuma tana fatan dawo da mu’amala da tattaunawa a fannoni daban-daban a tsakanin kasashen biyu cikin sauri. Ban da wannan kuma, bangaren Jamus yana mai da hankali sosai kan kiyaye tsarin samar da kayayyaki, bai amince da “mayar da wani bangare saniyar ware a fannin tattalin arziki” ba, kuma yana tsayawa tsayin dak kan nuna daidaito ga kamfanonin juna. (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsakanin Samari Da ‘Yan Mata, Wa Ya Kamata Ya Ba Wani ‘Ramadan Basket’

Next Post

Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

8 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

8 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

10 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

13 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

14 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

15 hours ago
Next Post
Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.