Ana zargin wani mutum mai suna Esosa Imasuen da dukan matarsa, Chinwedu Nnadozie, har ta mutu a birnin Benin na Jihar Edo.
Lamarin ya faru ne a titin Oza da ke unguwar Ogbelaka a kan hanyar Sakponba.
- Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna
- Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun
Wasu makusantan ma’auratan sun ce sun samu saÉ“ani, sai Esosa ya yi wa matarsa mugun duka, wanda ya jawo ta samu munanan raunuka.
Chinwedu, wadda ke da yara uku, an garzaya da ita asibiti inda likitoci suka gano tana fama da zubar jini a cikinta saboda tsananin dukan da aka yi mata.
Abin takaici, ta rasu kafin danginta su isa asibitin.
Mahaifinta, Everistus Nnadozie, ya ce an sanar da shi cewa surukinsa Esosa Imasuen ne ya yi wa ‘yarsa duka har ta samu raunika sosai.
Ya ƙara da cewa an kai ta asibiti inda likita ya tabbatar da cewa tana fama da zubar jini a cikin jikinta.
Ya ce kafin ya isa asibitin, ‘yarsa ta rasu.
Bayan haka kuma, Esosa ya É—auki gawarta ya kai wani waje ba tare da ya sanar da iyayenta ba.
“Na je gidansa, sai aka ce ya tsere,” in ji mahaifin.
Ya ce yana ta kiran Esosa domin ya nuna masa inda aka kai gawar ‘yarsa, amma ya Æ™i amsa waya.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Edo, ya ce sun duba wurare da dama a Benin, amma babu rahoton wannan lamari.
Ana ci gaba da neman Esosa Imasuen ruwa a jallo.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp