• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Jawabi Ya Nuna Dalilin Da Ya Sa Kasar Sin Ke Son Taimakawa Raya Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Wannan Jawabi Ya Nuna Dalilin Da Ya Sa Kasar Sin Ke Son Taimakawa Raya Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani jawabi a gaban kusan daukacin shugabannin kasashen Afirka, inda ya yi amfani da wani karin magana na Afirka wajen siffanta huldar dake tsakanin Sin da Afirka, wato “Mai buri daya shi ne aboki na gaske.”

 

A jawabin nan da shugaba Xi ya gabatar a bikin kaddamar da taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2024 da ke gudana a birnin Beijing na kasar Sin, shugaban ya ambaci buri daya da Sin da kasashen Afirka suke da shi, wato zamanantar da kansu.

  • An Zartas Da Sanarwar Beijing Da Tsarin Aiki A Taron FOCAC
  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude Taron Kolin FOCAC

Sai dai wane irin zamanantarwa ake bukata? A cewar shugaba Xi, ya kamata a yi kokarin samun zamanantarwa cikin adalci, da bude wa juna kofa da cin moriyar juna, da mai da jama’a a gaban kome, da kare muhallin halittu, da zaman lafiya da tsaro, da dai sauransu, kana kasar Sin na son hadin gwiwa da kasashen Afirka a wadannan fannoni. Daga baya, shugaban na kasar Sin ya gabatar da cikakken shirin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka na shekaru 3 masu zuwa, wanda ya shafi fannoni 10, da suka hada da cudanyar al’adu, da cinikayya, da tsarin masana’antu, da kayayyakin more rayuwa, da aikin gona, da dai makamantansu.

 

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Bayan da na saurari jawabin shugaba Xi, na ga jawabin ya nuna akidar Sin ta hadin gwiwa da kasashen Afirka, ta “gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da daukar hakikanan matakai”.

 

Don tabbatar da akidar, ya kamata a kula da moriyar kasashen Afirka. Hakika a cikin jawabin shugaba Xi, an ambaci dimbin matakan da za su haifar da moriya ga kasashen Afirka, misali “sanya kasashen Afirka samun karin riba bisa sarrafa kayayyaki” da “kara kwarewar kasashen Afirka wajen kiwon lafiya” da “taimakawa kasashen Afirka a kokarinsu na samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba” da dai sauransu.

 

Ban da haka, don aiwatar da akidar Sin a fannin hulda da kasashen Afirka, dole ne a aiwatar da matakan yadda ya kamata. A wannan fanni, za mu ga shirin da shugaba Xi Jinping ya ambata ya kunshi dimbin alkaluma, misali “ cikin shekaru 3 masu zuwa”, da “aiwatar da ayyukan hade kayayyakin more rayuwa 30”, da “tura kwararru masu ilimin aikin gona na zamani 500 zuwa nahiyar Afirka”, da “samar da akalla guraben aikin yi miliyan 1 ga mutanen Afirka”, da dai sauransu. Wadannan jimiloli an bayyana su sarai. Hakan ya nuna cewa za a iya aiwatar da matakan da aka tsara.

 

Sai dai watakila za ku so ku san dalilin da ya sa kasar Sin ke kula da moriyar kasashen Afirka, da neman taimakawa kasashen Afirka wajen cimma burinsu na zamanantar da kansu. Hakika jawabin shugaba Xi ya nuna dalilin da ya sa Sin yin haka, wanda ya kasance babbar manufar kasar ta fuskar hulda da kasashen waje, wato gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.

 

Mene ne ma’anar manufar? Idan mutane na wasu wurare sun samu rayuwa mai wadata da kwanciyar hankali, yayin da sauran mutane suka dade suna zama cikin yanayin talauci, da yunwa, har ma da yake-yake, to, wannan rashin daidaito tabbas zai haddasa rikici tsakanin gungun mutane, da lalacewar muhallin halittu, da rashin wani daidaitaccen tsari mai amfani a fannin kula da al’amuran duniya, da dai sauransu, wadanda za su haifar da barazana ga daukacin dan Adam. Saboda haka, an ce daukacin dan Adam na da makomar bai daya. Sa’an nan raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, na nufin sa kaimi ga hadin gwiwa don tabbatar da moriyar kowa, da neman ci gaban tattalin arziki na bai daya, tare da zummar sanya dukkan mutanen duniya samun zaman rayuwa mai inganci.

 

Kamar yadda shugaba Xi ya bayyana a cikin jawabinsa, “yawan al’ummar kasar Sin da ta nahiyar Afirka baki daya bisa yawan mutanen duniya, ya kai kashi daya cikin uku. Saboda haka, idan babu zamanantarwa a Sin da Afirka, ba za a samu zamanantarwar daukacin duniya ba.” Burin kasar Sin shi ne hadin gwiwa tare da kasashen Afirka a kokarinsu na zamanantar da kansu, ta yadda za a iya sa kaimi ga zamanantar da daukacin kasashe masu tasowa, gami da tabbatar da ci gaban dan Adam baki daya a karshe. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Dakatar Da Biyan Miliyan 10 Kuɗin Takarar Kujerar Shugaban Ƙaramar Hukuma A Kano

Next Post

Sin Za Ta Saukewa Kasashe Marasa Wadata Daukacin Harajin Da Suke Biya Kan Hajojin Cinikayyarsu

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

6 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 week ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 week ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

2 weeks ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 weeks ago
Next Post
Sin Za Ta Saukewa Kasashe Marasa Wadata Daukacin Harajin Da Suke Biya Kan Hajojin Cinikayyarsu

Sin Za Ta Saukewa Kasashe Marasa Wadata Daukacin Harajin Da Suke Biya Kan Hajojin Cinikayyarsu

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.