ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Jawabi Ya Nuna Dalilin Da Ya Sa Kasar Sin Ke Son Taimakawa Raya Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

A yau ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani jawabi a gaban kusan daukacin shugabannin kasashen Afirka, inda ya yi amfani da wani karin magana na Afirka wajen siffanta huldar dake tsakanin Sin da Afirka, wato “Mai buri daya shi ne aboki na gaske.”

 

A jawabin nan da shugaba Xi ya gabatar a bikin kaddamar da taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2024 da ke gudana a birnin Beijing na kasar Sin, shugaban ya ambaci buri daya da Sin da kasashen Afirka suke da shi, wato zamanantar da kansu.

ADVERTISEMENT
  • An Zartas Da Sanarwar Beijing Da Tsarin Aiki A Taron FOCAC
  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude Taron Kolin FOCAC

Sai dai wane irin zamanantarwa ake bukata? A cewar shugaba Xi, ya kamata a yi kokarin samun zamanantarwa cikin adalci, da bude wa juna kofa da cin moriyar juna, da mai da jama’a a gaban kome, da kare muhallin halittu, da zaman lafiya da tsaro, da dai sauransu, kana kasar Sin na son hadin gwiwa da kasashen Afirka a wadannan fannoni. Daga baya, shugaban na kasar Sin ya gabatar da cikakken shirin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka na shekaru 3 masu zuwa, wanda ya shafi fannoni 10, da suka hada da cudanyar al’adu, da cinikayya, da tsarin masana’antu, da kayayyakin more rayuwa, da aikin gona, da dai makamantansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Bayan da na saurari jawabin shugaba Xi, na ga jawabin ya nuna akidar Sin ta hadin gwiwa da kasashen Afirka, ta “gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da daukar hakikanan matakai”.

 

Don tabbatar da akidar, ya kamata a kula da moriyar kasashen Afirka. Hakika a cikin jawabin shugaba Xi, an ambaci dimbin matakan da za su haifar da moriya ga kasashen Afirka, misali “sanya kasashen Afirka samun karin riba bisa sarrafa kayayyaki” da “kara kwarewar kasashen Afirka wajen kiwon lafiya” da “taimakawa kasashen Afirka a kokarinsu na samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba” da dai sauransu.

 

Ban da haka, don aiwatar da akidar Sin a fannin hulda da kasashen Afirka, dole ne a aiwatar da matakan yadda ya kamata. A wannan fanni, za mu ga shirin da shugaba Xi Jinping ya ambata ya kunshi dimbin alkaluma, misali “ cikin shekaru 3 masu zuwa”, da “aiwatar da ayyukan hade kayayyakin more rayuwa 30”, da “tura kwararru masu ilimin aikin gona na zamani 500 zuwa nahiyar Afirka”, da “samar da akalla guraben aikin yi miliyan 1 ga mutanen Afirka”, da dai sauransu. Wadannan jimiloli an bayyana su sarai. Hakan ya nuna cewa za a iya aiwatar da matakan da aka tsara.

 

Sai dai watakila za ku so ku san dalilin da ya sa kasar Sin ke kula da moriyar kasashen Afirka, da neman taimakawa kasashen Afirka wajen cimma burinsu na zamanantar da kansu. Hakika jawabin shugaba Xi ya nuna dalilin da ya sa Sin yin haka, wanda ya kasance babbar manufar kasar ta fuskar hulda da kasashen waje, wato gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.

 

Mene ne ma’anar manufar? Idan mutane na wasu wurare sun samu rayuwa mai wadata da kwanciyar hankali, yayin da sauran mutane suka dade suna zama cikin yanayin talauci, da yunwa, har ma da yake-yake, to, wannan rashin daidaito tabbas zai haddasa rikici tsakanin gungun mutane, da lalacewar muhallin halittu, da rashin wani daidaitaccen tsari mai amfani a fannin kula da al’amuran duniya, da dai sauransu, wadanda za su haifar da barazana ga daukacin dan Adam. Saboda haka, an ce daukacin dan Adam na da makomar bai daya. Sa’an nan raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, na nufin sa kaimi ga hadin gwiwa don tabbatar da moriyar kowa, da neman ci gaban tattalin arziki na bai daya, tare da zummar sanya dukkan mutanen duniya samun zaman rayuwa mai inganci.

 

Kamar yadda shugaba Xi ya bayyana a cikin jawabinsa, “yawan al’ummar kasar Sin da ta nahiyar Afirka baki daya bisa yawan mutanen duniya, ya kai kashi daya cikin uku. Saboda haka, idan babu zamanantarwa a Sin da Afirka, ba za a samu zamanantarwar daukacin duniya ba.” Burin kasar Sin shi ne hadin gwiwa tare da kasashen Afirka a kokarinsu na zamanantar da kansu, ta yadda za a iya sa kaimi ga zamanantar da daukacin kasashe masu tasowa, gami da tabbatar da ci gaban dan Adam baki daya a karshe. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Sin Za Ta Saukewa Kasashe Marasa Wadata Daukacin Harajin Da Suke Biya Kan Hajojin Cinikayyarsu

Sin Za Ta Saukewa Kasashe Marasa Wadata Daukacin Harajin Da Suke Biya Kan Hajojin Cinikayyarsu

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.