ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Jawabi Ya Nuna Dalilin Da Ya Sa Kasar Sin Ke Son Taimakawa Raya Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

A yau ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani jawabi a gaban kusan daukacin shugabannin kasashen Afirka, inda ya yi amfani da wani karin magana na Afirka wajen siffanta huldar dake tsakanin Sin da Afirka, wato “Mai buri daya shi ne aboki na gaske.”

 

A jawabin nan da shugaba Xi ya gabatar a bikin kaddamar da taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2024 da ke gudana a birnin Beijing na kasar Sin, shugaban ya ambaci buri daya da Sin da kasashen Afirka suke da shi, wato zamanantar da kansu.

ADVERTISEMENT
  • An Zartas Da Sanarwar Beijing Da Tsarin Aiki A Taron FOCAC
  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude Taron Kolin FOCAC

Sai dai wane irin zamanantarwa ake bukata? A cewar shugaba Xi, ya kamata a yi kokarin samun zamanantarwa cikin adalci, da bude wa juna kofa da cin moriyar juna, da mai da jama’a a gaban kome, da kare muhallin halittu, da zaman lafiya da tsaro, da dai sauransu, kana kasar Sin na son hadin gwiwa da kasashen Afirka a wadannan fannoni. Daga baya, shugaban na kasar Sin ya gabatar da cikakken shirin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka na shekaru 3 masu zuwa, wanda ya shafi fannoni 10, da suka hada da cudanyar al’adu, da cinikayya, da tsarin masana’antu, da kayayyakin more rayuwa, da aikin gona, da dai makamantansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Bayan da na saurari jawabin shugaba Xi, na ga jawabin ya nuna akidar Sin ta hadin gwiwa da kasashen Afirka, ta “gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da daukar hakikanan matakai”.

 

Don tabbatar da akidar, ya kamata a kula da moriyar kasashen Afirka. Hakika a cikin jawabin shugaba Xi, an ambaci dimbin matakan da za su haifar da moriya ga kasashen Afirka, misali “sanya kasashen Afirka samun karin riba bisa sarrafa kayayyaki” da “kara kwarewar kasashen Afirka wajen kiwon lafiya” da “taimakawa kasashen Afirka a kokarinsu na samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba” da dai sauransu.

 

Ban da haka, don aiwatar da akidar Sin a fannin hulda da kasashen Afirka, dole ne a aiwatar da matakan yadda ya kamata. A wannan fanni, za mu ga shirin da shugaba Xi Jinping ya ambata ya kunshi dimbin alkaluma, misali “ cikin shekaru 3 masu zuwa”, da “aiwatar da ayyukan hade kayayyakin more rayuwa 30”, da “tura kwararru masu ilimin aikin gona na zamani 500 zuwa nahiyar Afirka”, da “samar da akalla guraben aikin yi miliyan 1 ga mutanen Afirka”, da dai sauransu. Wadannan jimiloli an bayyana su sarai. Hakan ya nuna cewa za a iya aiwatar da matakan da aka tsara.

 

Sai dai watakila za ku so ku san dalilin da ya sa kasar Sin ke kula da moriyar kasashen Afirka, da neman taimakawa kasashen Afirka wajen cimma burinsu na zamanantar da kansu. Hakika jawabin shugaba Xi ya nuna dalilin da ya sa Sin yin haka, wanda ya kasance babbar manufar kasar ta fuskar hulda da kasashen waje, wato gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya.

 

Mene ne ma’anar manufar? Idan mutane na wasu wurare sun samu rayuwa mai wadata da kwanciyar hankali, yayin da sauran mutane suka dade suna zama cikin yanayin talauci, da yunwa, har ma da yake-yake, to, wannan rashin daidaito tabbas zai haddasa rikici tsakanin gungun mutane, da lalacewar muhallin halittu, da rashin wani daidaitaccen tsari mai amfani a fannin kula da al’amuran duniya, da dai sauransu, wadanda za su haifar da barazana ga daukacin dan Adam. Saboda haka, an ce daukacin dan Adam na da makomar bai daya. Sa’an nan raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, na nufin sa kaimi ga hadin gwiwa don tabbatar da moriyar kowa, da neman ci gaban tattalin arziki na bai daya, tare da zummar sanya dukkan mutanen duniya samun zaman rayuwa mai inganci.

 

Kamar yadda shugaba Xi ya bayyana a cikin jawabinsa, “yawan al’ummar kasar Sin da ta nahiyar Afirka baki daya bisa yawan mutanen duniya, ya kai kashi daya cikin uku. Saboda haka, idan babu zamanantarwa a Sin da Afirka, ba za a samu zamanantarwar daukacin duniya ba.” Burin kasar Sin shi ne hadin gwiwa tare da kasashen Afirka a kokarinsu na zamanantar da kansu, ta yadda za a iya sa kaimi ga zamanantar da daukacin kasashe masu tasowa, gami da tabbatar da ci gaban dan Adam baki daya a karshe. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Sin Za Ta Saukewa Kasashe Marasa Wadata Daukacin Harajin Da Suke Biya Kan Hajojin Cinikayyarsu

Sin Za Ta Saukewa Kasashe Marasa Wadata Daukacin Harajin Da Suke Biya Kan Hajojin Cinikayyarsu

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.