• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Abubuwa Da Ya Kamata A Sani Game Da Manyan Taruka Biyu Da Za A Yi A Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Kasar Sin
0
Wasu Abubuwa Da Ya Kamata A Sani Game Da Manyan Taruka Biyu Da Za A Yi A Kasar Sin

Ga yadda kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ya yi bayani ga manema labaru kan rahoton da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya gabatar a yayin bikin kaddamar da babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranakun 4 da 5 ga watan Maris na bana, za a gudanar da tarukan kasa guda biyu a nan kasar Sin, wato cikakken zama karo na farko na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa na jama’ar kasar Sin karo na 14, da kuma cikakken zama karo na farko na babban taron wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14 bi da bi.
Ajandar babban taron wakilan jama’ar kasar Sin na wannan karo, shi ne duba rahoto game da yadda gwamnatin kasar Sin ta sauke nauyin dake biya wuyanta a bara, da aikin da za ta yi a bana. Sannan wakilan jama’a za su duba rahoto kan yadda aka aiwatar da shirin raya tattalin arzikin kasa da ci gaban jama’a na shekarar 2022 da daftarin shirin raya tattalin arziki da zamantakewar kasa na shekarar 2023, da daftarin tattalin arzikin kasa na shekarar 2023, da shirin ci gaban zamantakewa, da kuma nazarin tsarin tattalin arziki da ci gaban zamantakewar al’umma, da duba rahoton aiki na zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’a, duba rahoton aiki na kotun koli, duba rahoton aiki na majalisar koli ta jama’a, zabe da kuma nada sabbin jami’an hukumomin gwamnatin kasar Sin, kamar su firaministan gwamnatin kasar, da mataimakansa da ministocin gwamnati, da dai sauransu.

Ajandar taron kwamitin ba da shawara kan harkokin siyasa na jama’ar kasar Sin shi ne saurara da duba rahoton ayyukan zaunannen kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama’ar kasar Sin, da rahoton ayyukan shawarwari, dubawa da zartas da gyaran kundin sauraran shawarwari na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasar kasar Sin, ya kuma zabi shugaba da mataimakansa da babban sakatare da mambobin zaunanen kwamitin na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa na jama’ar kasar Sin karo na 14 da dai sauransu.

Akwai sabbin abubuwa da yawa a cikin tarukan kasa guda biyu na wannan karo, wanda ke jan hankalin jama’a a duk fadin kasar. A siyasance, sabbin wakilan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin da mambobin kwamitin ba da shawara kan harkokin siyasa na jama’ar kasar Sin za su halarci tarukan biyu. A lokacin, wakilai da ’yan kwamiti daga wuraren kasar daban daban za su gudanar da ayyukansu, kana za su tuntubi juna da ba da shawarwarinsu. A sa’i daya kuma, yayin da aka fitar da jerin sunayen “manyan shugabanni” da tawagogin jagoranci na cibiyoyi daban daban, fagen siyasar kasar Sin zai kammala mika mulki tare da kafa wani sabon layi. Kamar yadda aka saba, sabon firaministan kasar Sin da mataimakin firaministan majalisar gudanarwar kasar Sin, za su fito fili don ganawa da ‘yan jaridun kasar Sin da na kasashen waje. A madadin sabuwar gwamnatin tsakiya, sabon firaministan zai amsa tambayoyi daga manema labarai, da gabatar da manufofin da kuma mayar da martani ga tsammanin jama’a.

•Beijing, dandalin Tiananmen ya bude mabubbugan ruwa don maraba da tarukan kasa biyu

Ta fuskar tattalin arziki, yadda za a tsara ingantaccen ci gaba a cikin rahoton ayyukan gwamnati na wannan shekara, musamman ma abin da aka sa a gaba ga tattalin arzikin kasar a shekarar 2023, ya cancanci a ci gaba da kula da su. A game da rayuwar jama’a, sabon kwamitin wakilan zai tattauna batutuwan da suka shafi tattalin arzikin kasa da rayuwar jama’a, da tabbatar da burin jama’a na samun ingantacciyar rayuwa a hakika, da rubuta wani sabon labari game da dimokradiyyar kasar Sin. A fannin yin gyare gyare da bude kofa ga waje, bana shekara ce ta cika shekaraku 45 da gudanar da manufar yin gyare gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje ta kasar Sin, kana sabbin matakan gyare gyare da bude kofa ga kasashen waje da kasar Sin ta dauka sun jawo hankalin duniya baki daya. Wadanne irin matakan bude ido ne majalisar wakilan jama’ar kasar za ta dauka a bana cike da fata?

Ta fuskar diflomasiyya, shugaban kasar Philippines, da shugaban Turkmenistan, da firaministan Kambodia, da shugaban kasar Iran sun ziyarci kasar Sin cikin nasara, dangantakar diflomasiyya tsakanin shugabannin kasa da kasa ta fara shiga wani sabon matsayi a farkon wannan shekara. Shekarar bana ta zo daidai da cika shekaru 10 da gudanar da shawarar “Ziri daya da hanya daya”, kuma yadda kasar Sin za ta ba da labarin hadin gwiwa kan “berin raya kasa” da “hanyar farin ciki” a harkokin diflomasiyyar cikin gida shi ma zai jawo hankalin jama’a. Bugu da kari, wannan shekara ita ce karon farko da sabon ministan harkokin wajen kasar Sin zai bayyana a tarukan biyu bayan kama aiki. Ta hanyar lura da taron manema labarai na ministan harkokin wajen kasar, kasashen waje na iya samun dan karamin ilimi da karin haske kan sabbin hanyoyin da ake bi na diflomasiyyar manyan kasashe.

Labarai Masu Nasaba

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

Yadda tsarin dimokuradiyya irin na kasar Sin ke aiki yadda ya kamata, da tarukan kasa guda biyu, za su ba da wani kyakkyawan misali ga kasashen waje. A cikin tsarin kasar Sin, tarukan kasa guda biyu na kasar Sin sun kasance muhimman abubuwa wajen aiwatar da tsarin dimokuradiyyar jama’a a dukkan matakai, kuma wannan shi ne cikakken tsarin dimokuradiyyar jama’a a dukkan matakai.

Tsarin dimokuradiyyar jama’a a dukkan matakai wani takaitaccen bayani ne na tsarin dimokuradiyya na jama’ar kasar Sin, tsarin dimokuradiyyar jama’a a dukkan matakai yana bin ka’ida ta tsakiya da jama’a ta farko, kuma wani salo ne na siyasa da dukkan jama’a za su iya shiga cikinta. Babban sakatare na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping ya jaddada cewa, ya zama wajibi a samar da cikakken tsari na hukumomi da gudanar da ayyukan hadin gwiwa, domin tabbatar da cewa jama’a na da ‘yancin shiga ana damawa da su, da ci gaba da zurfafa harkokin siyasa na yau da kullum.

•Ga yadda tattabarai suka tashi a ranar farko ta sabuwar shekarar 2023 a filin Tian’anmen dake cikin

Dimokuradiyyar “jama’a” ita ma wata muhimmiyar alama ce da ke banbance dimokuradiyyar gurguzu mai tsarin musamman ta kasar Sin da dimokuradiyya irin ta nahiya Turai. Duk da cewa dimokuradiyya irin ta kasashen yamma ita ma tana tallata “ ‘yancin jama’a”, a aikace, da wuya a iya tabbatar da ‘yancin siyasa na mutane masu karamin karfi, abu ne mai wahala a mayar da ra’ayoyin dake shafar moriyarsu zuwa manufofi na hakika, ko da ya zama manufa, yana da wuya a aiwatar da shi yadda ya kamata.
A shekarar 2019, babban sakatare Xi Jinping ya ba da shawara a karon farko cewa, “tsarin demokiradiya da ya shafi al’umma baki daya”. A cikin daftarin gyare gyaren da aka yi wa dokar dabi’ar majalisar wakilan jama’ar kasar Sin da ka’idojin gudanarwa na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin da aka zartar a watan Maris na shekarar 2021, an rubuta “tsarin demokiradiya da ya shafi al’umma baki daya” a fili.

A cikin watan Oktoba na shekarar 2022, rahoton babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20 ya bayyana cewa,bunkasa “tsarin demokiradiya da ya shafi al’umma baki daya”, wani muhimmin abu ne da yake kunshe cikin muhimman bukatu wajen zamanantar da kasar Sin, ya kuma jaddada cewa, tsarin dimokuradiyyar jama’a a dukkan matakai shi ne muhimmiyyar siffa ta siyasar dimokuradiyyar gurguzu, kuma gabatar da wasu bukatu wajen bunkasa dimokuradiyyar jama’a a dukkan matakai da kuma tabbatar da cewa jama’a su ne masu mulkin kasar nan. Wannan yana da ma’ana mai girma ga sabon zamani da sabuwar tafiya don kara yin amfani da moriyar tsarin siyasar gurguzu na kasar Sin, da gina kasa mai ra’ayin gurguzu ta zamani baki daya, da sa kaimi ga ci gaban babban farfadowar al’ummar kasar Sin.

Don bunkasa dimokuradiyyar jama’a a dukkan matakai, kamata ya yi a ba da cikakken dama ga muhimmiyar rawar da tsarin majalisar wakilan jama’a ke takawa, muna bukatar yin aiki mai kyau a cikin wadannan bangarori. Na farko shi ne tabbatar da shugabancin jam’iyyar, jama’a su ne masu mulkin kasar nan, da bin doka da oda, a ci gaba da fadada shigar jama’a a siyasance, da tabbatar da cewa jama’a sun samu ‘yancin walwala da dama kamar yadda doka ta tanada.

Beijing, an kada jajayen tutoci a filin Tian’anmen dake cikin garin Beijing

Na biyu shi ne aiwatar da cibiyoyi da hanyoyin da suka dace na kundin tsarin mulki da dokoki kan dimokuradiyya, da kuma amfani da tsare-tsare na kimiyya da inganci don tabbatar da cewa an aiwatar da ka’idojin da kundin tsarin mulki da dokoki suka kafa da kuma kiyaye martabar dokokin kasar.

Na uku shi ne, kyautata tsarin shari’ar gurguzu mai siffar kasar Sin, da ta taka cikakken rawa wajen jagorancin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin da zaunannen kwamitinta kan ayyukan kafa dokoki, da kiyaye doka ga jama’a, da dogara ga jama’a, da amfanar da jama’a, da kuma kare jama’a, da kuma kara inganta dokoki na kimiyya da dimokuradiyya don inganta ci gaba bisa dokoki masu kyau.

Na hudu shi ne karfafa sa ido kan majalissar wakilan jama’a don tabbatar da aiwatar da dokoki da ka’idoji yadda ya kamata.

Na biyar shi ne ba da cikakken dama ga aikin majalisar wakilan jama’a, kulla alaka ta kut da kut da jama’a, sauraron ra’ayoyi da shawarwarin jama’a, yarda da kulawar jama’a, karfafa karfin wakilai, da kuma ƙoƙarin yi wa jama’a hidima.

Na shida shi ne inganta dandalin bayyana ra’ayoyin jama’a na dimokuradiyya na majalisar wakilan jama’ar kasar, da inganta tsarin aiki na karbar ra’ayin jama’a da hada hikimar jama’a. Na bakwai shi ne karfafa wayar da kan jama’a game da harkokin siyasa, da kokarin gina wata tawaga ta ‘yan majalisar jama’a masu tsayin daka a siyasance, masu yi wa jama’a hidima, mutunta doka, da kuma inganta dimokuradiyya, ta yadda za a bayar da sababbin gudunmawa ga ci gaban dimokuradiyyar jama’a a kan bunkasa tsarin dimokuraddiyar jama’a a dukkan matakai da kuma tabbatar da cewa jama’a su ne masu mulkin kasar.

Wata harabar babban dakin taro na jama’a na Beijing, inda ake tattauna harkokin siyasa na kasar Sin

A shekarar 2022, an yi nasarar gudanar da babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20, inda aka zana wani babban tsari na gina kasa mai bin tsarin gurguzu ta zamani bisa daga dukkan fannoni, da kuma sa kaimi ga babban farfagandar al’ummar kasar Sin tare da zamanantar da kasar Sin. A cikin sabuwar shekara, tarukan kasa guda biyu za su sake yin wata sabuwar tafiya, da yada ra’ayoyin jama’a, da tattara ra’ayoyinsu, da tattara karfinsu, da kuma ci gaba da busa kiraye-kirayen zamani na sabuwar tafiya. (Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Wajen Sin Ya Bukaci Dunkulewar Duniya Mai Inganci A Taron G20

Next Post

Gwagwarmayar Siyasar Tinubu

Related

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
Daga Kasar Sin

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

2 months ago
Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin
Daga Kasar Sin

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

10 months ago
wang lili
Daga Kasar Sin

Yadda Wang Lili Ke Kiyaye Neman Cimma Nasara A Wasan Kwallon Kwando

10 months ago
Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura
Daga Kasar Sin

Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura

11 months ago
Zambiya
Daga Kasar Sin

’Yar Kasar Zambiya: A Nan Kasar Sin, Ina Jin Tamkar Ina Gida!

1 year ago
Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin
Daga Kasar Sin

Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin

1 year ago
Next Post
Tinubu

Gwagwarmayar Siyasar Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.