• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (3)

by Bilkisu Tijjani
8 months ago
in Adon Gari
0
Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi-Dasilba

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi-Dasilba
Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi shahararriyar a shafukan sada zaumunta mai yada labarai, mai bayar da shawara akan abin ya shafi jinsi, kuma kwararriya kan harkokin sadarwa tare da maida hankali kan sabbin kafafen yada labarai da dabarun sadarwa. A matsayinta na wanda ta kafa kungiyar Not Too Young ToRun Mobement, ta taka rawar gani wajen kokari karfafawa matasa gwiwa a harkokin siyasa, da bayar da shawarwarin daidaita jinsi, da bai wa matasa damar taka rawar gani a harkokin mulki.

Maryam ta shahara sosai wajen kokarin da take yi na inganta shigar mata a fagen siyasa da kuma kara daukaka muryar kungiyoyin da aka ware. Ita ce shugabar 00 na yau da kullun akan tattaunawar kwamiti kuma akai-akai tana hidima a matsayin mai ba da shawara, kuma mai kula da al’amuran zamantakewa da na sana’a.

Shawararta har ta wuce magana da jama’a ta kai ga rubuce-rubuce da ayyukanta na sadaukarwa, ta ci gaba da wayar da kan jama’a game da daidaiton jinsi, adalcin zamantakewa, da shigar da matasa a cikin harkokin siyasa, wanda hakan ya sa ta zama daya daga cikin masu fada a ji a fagen gwagwarmayar samar da al’umma mai hade da adalci.

Joana Nnazua Kolo

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Arewa

Joana Nnazua Kolo ta kasance mai ba da agajin jin kai wadda ta kafa tarihi a matsayin kwamishiniya mafi karancin shekaru a Nijeriya tana da shekaru 26.

An nada ta mukamin kwamishiniya mai Kula Da Harkokin Matasa da Wasanni a Jihar Kwara kafin makonni biyu kacal ta kammala Bautar kasar ta (NYSC) a watan Oktoban 2019, inda ta koyar a makarantar sakandare ta Model Boarding Junior da ke Garin Guri, a Jihar Jigawa.

An san Joana saboda sadaukar da kai ga ayyukan jin kai, ci gaban al’umma, da bayar da shawarwari don samar da shugabanci na gari, an nada Joana tana daya daga cikin “Manyan Mata 100 Mafi Tasiri” a Jaridar Guardian cikin 2020. Ta kuma zama mai ba da shawara kan karfafawa yara ‘yan mata shawara ga Gwamnan Jihar Kwara, tare da yin amfani da kokarinta na fafutukar kare hakkin mata matasa da samar da canji mai karfi a cikin al’ummarta.

Maryam Booth

Arewa

Maryam Ado Mohammed, wacce aka fi sani da Maryam Booth, ita shahararriyar jaruma a tsangayar Kannywood wacce ta yi wani abin burgewa wanda ta yi fice saboda kwazonta a cikin The Milkmaid (2020), an ba ta babbar lambar yabo ta Africa Mobie Academy Award a matsayin mafi kyawun jarumai a cikin rawar da ta taka.

Baya ga nasarorin da ta samu a harkar fim, an nada Maryam a matsayin jakadiyar abinci ta Sumal a shekarar 2022, wanda ya kara tabbatar da tasirinta. Ita ma kwakkwaran ‘yar kasuwa ce kuma wacce ta kafa MBooth Beauty Parlour, ta jajirce wajen karfafa wasu ta hanyar kasuwancinta.

Maryam Uwais

Arewa

Maryam Uwais fitacciyar lauya ce, sannan kuma ’yar kasuwa, kuma mai kokarin kare hakkin dan’Adam, ta kasance ta ba da gudunmawa sosai wajen saka hannun jari da kuma rage radadin talauci a Nijeriya. Daga shekarar 2015 zuwa 2023, ta yi aiki a matsayin mai ba wa shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara na musamman kan harkokin zuba jari, inda ta taka rawar gani wajen tsarawa da aiwatar da shirin nan na ‘National Social Inbestment Programs (NSIP),’ da ke da nufin rage radadin fatara da talauci a tsakanin al’umma marasa galihu ta hanyar zamantakewa.

Ta shafe sama da shekaru 36 tana aikin shari’a, Maryam ta rike manyan mukamai a ma’aikatar masana’antu ta Jihar Kano, da Babban Bankin Nijeriya, da kuma hukumar gyara dokokin Nijeriya. Ta kuma yi aiki a matsayin mai ba da rahoto na musamman kan hakkin yara ga Hukumar Kare Hakkin dan Adama ta kasa kuma ta kafa shirin Isa Wali Empowerment Initiatibe a 2009 don magance matsalolin mata da farin cikin yara. Maryam ta samu da kyautuka da dama da suka hada da lambar yabo na mata masu jaruntaka na duniya da lambar yabo ta mata wadanda suka jagoranci ci gaban zamantakewar al’umma a shekarar 2022.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaFiceMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Ƙudiri Nema Wa Arewa Mafita – Shekarau

Next Post

Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (11)

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

1 month ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

2 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

5 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

5 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

6 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

6 months ago
Next Post
Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (11)

Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (11)

LABARAI MASU NASABA

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

June 24, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

June 24, 2025
Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC

Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC

June 24, 2025
An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan ÆŠaurin Aure A Filato – Uba Sani

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan ÆŠaurin Aure A Filato – Uba Sani

June 24, 2025
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don ÆŠaukar Mbeumo Daga Brentford

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don ÆŠaukar Mbeumo Daga Brentford

June 24, 2025
Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

June 24, 2025
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

June 24, 2025
Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

June 23, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

June 23, 2025
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.