• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (3)

by Bilkisu Tijjani
7 months ago
in Adon Gari
0
Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi-Dasilba

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi-Dasilba
Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi shahararriyar a shafukan sada zaumunta mai yada labarai, mai bayar da shawara akan abin ya shafi jinsi, kuma kwararriya kan harkokin sadarwa tare da maida hankali kan sabbin kafafen yada labarai da dabarun sadarwa. A matsayinta na wanda ta kafa kungiyar Not Too Young ToRun Mobement, ta taka rawar gani wajen kokari karfafawa matasa gwiwa a harkokin siyasa, da bayar da shawarwarin daidaita jinsi, da bai wa matasa damar taka rawar gani a harkokin mulki.

Maryam ta shahara sosai wajen kokarin da take yi na inganta shigar mata a fagen siyasa da kuma kara daukaka muryar kungiyoyin da aka ware. Ita ce shugabar 00 na yau da kullun akan tattaunawar kwamiti kuma akai-akai tana hidima a matsayin mai ba da shawara, kuma mai kula da al’amuran zamantakewa da na sana’a.

Shawararta har ta wuce magana da jama’a ta kai ga rubuce-rubuce da ayyukanta na sadaukarwa, ta ci gaba da wayar da kan jama’a game da daidaiton jinsi, adalcin zamantakewa, da shigar da matasa a cikin harkokin siyasa, wanda hakan ya sa ta zama daya daga cikin masu fada a ji a fagen gwagwarmayar samar da al’umma mai hade da adalci.

Joana Nnazua Kolo

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

Arewa

Joana Nnazua Kolo ta kasance mai ba da agajin jin kai wadda ta kafa tarihi a matsayin kwamishiniya mafi karancin shekaru a Nijeriya tana da shekaru 26.

An nada ta mukamin kwamishiniya mai Kula Da Harkokin Matasa da Wasanni a Jihar Kwara kafin makonni biyu kacal ta kammala Bautar kasar ta (NYSC) a watan Oktoban 2019, inda ta koyar a makarantar sakandare ta Model Boarding Junior da ke Garin Guri, a Jihar Jigawa.

An san Joana saboda sadaukar da kai ga ayyukan jin kai, ci gaban al’umma, da bayar da shawarwari don samar da shugabanci na gari, an nada Joana tana daya daga cikin “Manyan Mata 100 Mafi Tasiri” a Jaridar Guardian cikin 2020. Ta kuma zama mai ba da shawara kan karfafawa yara ‘yan mata shawara ga Gwamnan Jihar Kwara, tare da yin amfani da kokarinta na fafutukar kare hakkin mata matasa da samar da canji mai karfi a cikin al’ummarta.

Maryam Booth

Arewa

Maryam Ado Mohammed, wacce aka fi sani da Maryam Booth, ita shahararriyar jaruma a tsangayar Kannywood wacce ta yi wani abin burgewa wanda ta yi fice saboda kwazonta a cikin The Milkmaid (2020), an ba ta babbar lambar yabo ta Africa Mobie Academy Award a matsayin mafi kyawun jarumai a cikin rawar da ta taka.

Baya ga nasarorin da ta samu a harkar fim, an nada Maryam a matsayin jakadiyar abinci ta Sumal a shekarar 2022, wanda ya kara tabbatar da tasirinta. Ita ma kwakkwaran ‘yar kasuwa ce kuma wacce ta kafa MBooth Beauty Parlour, ta jajirce wajen karfafa wasu ta hanyar kasuwancinta.

Maryam Uwais

Arewa

Maryam Uwais fitacciyar lauya ce, sannan kuma ’yar kasuwa, kuma mai kokarin kare hakkin dan’Adam, ta kasance ta ba da gudunmawa sosai wajen saka hannun jari da kuma rage radadin talauci a Nijeriya. Daga shekarar 2015 zuwa 2023, ta yi aiki a matsayin mai ba wa shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara na musamman kan harkokin zuba jari, inda ta taka rawar gani wajen tsarawa da aiwatar da shirin nan na ‘National Social Inbestment Programs (NSIP),’ da ke da nufin rage radadin fatara da talauci a tsakanin al’umma marasa galihu ta hanyar zamantakewa.

Ta shafe sama da shekaru 36 tana aikin shari’a, Maryam ta rike manyan mukamai a ma’aikatar masana’antu ta Jihar Kano, da Babban Bankin Nijeriya, da kuma hukumar gyara dokokin Nijeriya. Ta kuma yi aiki a matsayin mai ba da rahoto na musamman kan hakkin yara ga Hukumar Kare Hakkin dan Adama ta kasa kuma ta kafa shirin Isa Wali Empowerment Initiatibe a 2009 don magance matsalolin mata da farin cikin yara. Maryam ta samu da kyautuka da dama da suka hada da lambar yabo na mata masu jaruntaka na duniya da lambar yabo ta mata wadanda suka jagoranci ci gaban zamantakewar al’umma a shekarar 2022.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaFiceMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Ƙudiri Nema Wa Arewa Mafita – Shekarau

Next Post

Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (11)

Related

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

1 week ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

3 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

4 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

5 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

5 months ago
Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad
Adon Gari

Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

6 months ago
Next Post
Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (11)

Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (11)

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.