• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (3)

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi-Dasilba
Maryam Laushi-Dasilba

Maryam Laushi shahararriyar a shafukan sada zaumunta mai yada labarai, mai bayar da shawara akan abin ya shafi jinsi, kuma kwararriya kan harkokin sadarwa tare da maida hankali kan sabbin kafafen yada labarai da dabarun sadarwa. A matsayinta na wanda ta kafa kungiyar Not Too Young ToRun Mobement, ta taka rawar gani wajen kokari karfafawa matasa gwiwa a harkokin siyasa, da bayar da shawarwarin daidaita jinsi, da bai wa matasa damar taka rawar gani a harkokin mulki.

Maryam ta shahara sosai wajen kokarin da take yi na inganta shigar mata a fagen siyasa da kuma kara daukaka muryar kungiyoyin da aka ware. Ita ce shugabar 00 na yau da kullun akan tattaunawar kwamiti kuma akai-akai tana hidima a matsayin mai ba da shawara, kuma mai kula da al’amuran zamantakewa da na sana’a.

Shawararta har ta wuce magana da jama’a ta kai ga rubuce-rubuce da ayyukanta na sadaukarwa, ta ci gaba da wayar da kan jama’a game da daidaiton jinsi, adalcin zamantakewa, da shigar da matasa a cikin harkokin siyasa, wanda hakan ya sa ta zama daya daga cikin masu fada a ji a fagen gwagwarmayar samar da al’umma mai hade da adalci.

Joana Nnazua Kolo

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Arewa

Joana Nnazua Kolo ta kasance mai ba da agajin jin kai wadda ta kafa tarihi a matsayin kwamishiniya mafi karancin shekaru a Nijeriya tana da shekaru 26.

An nada ta mukamin kwamishiniya mai Kula Da Harkokin Matasa da Wasanni a Jihar Kwara kafin makonni biyu kacal ta kammala Bautar kasar ta (NYSC) a watan Oktoban 2019, inda ta koyar a makarantar sakandare ta Model Boarding Junior da ke Garin Guri, a Jihar Jigawa.

An san Joana saboda sadaukar da kai ga ayyukan jin kai, ci gaban al’umma, da bayar da shawarwari don samar da shugabanci na gari, an nada Joana tana daya daga cikin “Manyan Mata 100 Mafi Tasiri” a Jaridar Guardian cikin 2020. Ta kuma zama mai ba da shawara kan karfafawa yara ‘yan mata shawara ga Gwamnan Jihar Kwara, tare da yin amfani da kokarinta na fafutukar kare hakkin mata matasa da samar da canji mai karfi a cikin al’ummarta.

Maryam Booth

Arewa

Maryam Ado Mohammed, wacce aka fi sani da Maryam Booth, ita shahararriyar jaruma a tsangayar Kannywood wacce ta yi wani abin burgewa wanda ta yi fice saboda kwazonta a cikin The Milkmaid (2020), an ba ta babbar lambar yabo ta Africa Mobie Academy Award a matsayin mafi kyawun jarumai a cikin rawar da ta taka.

Baya ga nasarorin da ta samu a harkar fim, an nada Maryam a matsayin jakadiyar abinci ta Sumal a shekarar 2022, wanda ya kara tabbatar da tasirinta. Ita ma kwakkwaran ‘yar kasuwa ce kuma wacce ta kafa MBooth Beauty Parlour, ta jajirce wajen karfafa wasu ta hanyar kasuwancinta.

Maryam Uwais

Arewa

Maryam Uwais fitacciyar lauya ce, sannan kuma ’yar kasuwa, kuma mai kokarin kare hakkin dan’Adam, ta kasance ta ba da gudunmawa sosai wajen saka hannun jari da kuma rage radadin talauci a Nijeriya. Daga shekarar 2015 zuwa 2023, ta yi aiki a matsayin mai ba wa shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara na musamman kan harkokin zuba jari, inda ta taka rawar gani wajen tsarawa da aiwatar da shirin nan na ‘National Social Inbestment Programs (NSIP),’ da ke da nufin rage radadin fatara da talauci a tsakanin al’umma marasa galihu ta hanyar zamantakewa.

Ta shafe sama da shekaru 36 tana aikin shari’a, Maryam ta rike manyan mukamai a ma’aikatar masana’antu ta Jihar Kano, da Babban Bankin Nijeriya, da kuma hukumar gyara dokokin Nijeriya. Ta kuma yi aiki a matsayin mai ba da rahoto na musamman kan hakkin yara ga Hukumar Kare Hakkin dan Adama ta kasa kuma ta kafa shirin Isa Wali Empowerment Initiatibe a 2009 don magance matsalolin mata da farin cikin yara. Maryam ta samu da kyautuka da dama da suka hada da lambar yabo na mata masu jaruntaka na duniya da lambar yabo ta mata wadanda suka jagoranci ci gaban zamantakewar al’umma a shekarar 2022.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

August 31, 2025
Next Post
Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (11)

Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (11)

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.