• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu ‘Yan Majalisa Da Suka Shafe Shekaru Masu Yawa A Kujera

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Majalisa

Tun bayan dawowar dimokuradiyya Nijeriya a shekarar 1999, daruruwan mutane sun wakilci al’umma a mazabunsu daban-daban.

Su ‘yan majalisa ba su da ka’idar wa’adin mulki kamar yadda shugaban kasa ko gwamna ke da damar shugabanci har sau biyu ma’ana shekara 8. Hakan ya sanya wasu suke samun damar daukan shekaru masu yawan gaske a zauren majalisar tarayyar Nijeriya.

  • NNPP Ta Yi Sabbin Kamu A Jihar Kaduna

A nan ga wasu ‘yan majalisan kasa da suka kwashe sherkaru masu yawa a zauren majalisan tarayyar Nijeriya.

Nicholas Mutu
Tun da aka dawo mulkin farar hula a shekarar 1999, Hon. Nicholas Mutu ne yake wakiltar mutanen Bomadi/Patani na Jihar Delta a majalisar tarayya. Nicholas Mutu ya rike shugabancin kwamitin kula da hukumar bunkasa yankin Neja Delta tun daga 2009 har zuwa 2019.

Ahmad Lawan
A zaben 1999 ne Ahmad Ibrahim Lawan ya zama dan majalisar wakilai, mai wakiltar yankin Bade/Jakusko. A wannan kujera ne ya yi shekara takwas a karkashin jam’iyyar ANPP har zuwa 2007. A zaben na 2007 ne Ahmad Lawan ya zama Sanatan Arewacin Jihar Yobe. A 2019, ya karbi shugabancin majalisar dattawan Nijeriya har zuwa yau.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Femi Gbajabiamila
Femi Gbajabiamila shi ne shugaban majalisar wakilan tarayya na kasa a yau. Dan siyasan yana kan wa’adinsa na biyar kenan a kujerar majalisa. A 2003, Femi Gbajabiamila ya zama dan majalisar yankin Surulere I, tun wancan lokaci bai fadi zabe ba. Bayan shekara 16 ya zama mutum na hudu a kasar nan.

Muhammad Ali Ndume
Shi ma Muhammad Ali Ndume ya zama dan majalisar wakilai na yankin Chibok/Damboa/Gwoza ne a 2003, ya yi shekara takwas yana rike da wannan mukami. A 2011 aka zabe shi a matsayin Sanatan Kudancin Borno, har yau kuma shi ne a kan kujerar.

Ike Ekweremadu
Ba a taba yin wanda ya dade yana jagorantar majalisar dattawa kamar Sanata Ike Ekweremadu ba. Shi ma ya zo majalisa ne a 2003, kuma ya dade ana yi da shi. Ike Ekweremadu ya shafe shekaru 12 a jere a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa. Wanda shi ne ya fi dadewa a mukami a zauren majalisa.

James Manager
Ba zai yiwu a yi maganar santaocin da suka dade ba tare da an ambaci James Manager ba. Sanatan zai cika shekara 20 yana wakiltar mutanen kudancin Delta a 2023.

Leo Ogor
Wani dan siyasa da ya tare a majalisar tarayya Nijeriya tun 2003 shi ne Leo Ogor. A shekara mai zuwa dan majalisar na Isoko-North/Isoko-South zai cika shekara 20.

Alhassan Ado-Doguwa
Shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai, Alhassan Ado-Doguwa ya zo majalisa ne a 2007. Ana tunanin yana harin shugaban majalisa idan ya zarce a 2023. Shi ne dan majalisa na farko a tarihin Nijeriya wanda yana kammala bautar kasarsa aka rantsar da shi majalisa.

Mohammed Monguno
Wani wanda ya dade a majalisa kuma yana neman shugabanci shi ne Hon. Mohammed Monguno mai wakiltar Marte/Monguno/Nganzai, sau biyar ana rantsar da shi.

Kabiru Ibrahim Gaya
A shekarar 2007 ne Kabiru Ibrahim Gaya ya zama Sanatan Kudancin Kano a majalisar dattawa. Tsohon gwamnan Jihar Kano ne a jamhoriya ta uku karkashin rusasshiyar jam’iyyar NRC. A zabe mai zuwa shi ne zai sake tsaya wa jam’iyyar APC takara a Kano.

Enyinnaya Abaribe
Bayan rikicinsa da Gwamnansa a 2007, Enyinnaya Abaribe ya zama Sanatan Abiya ta Kudu a majalisa, shekararsa 15 kenan bai motsa daga majalisar dattawan ba. A 1999 shi ne mataimakin gwamnan Jihar Abiya.

Yakubu Dogara
Tsohon shugaban majaliar wakilai Yakubu Dogara yana cikin wadanda suka ga jiya da yau a majalisa, tun 2007 yake wakiltar Bogoro, Dass da Tafawa Balewa. Ya yi shugaban masu rinjaye da shugaban marasa rinjaye a zauren majalisar.

Mukhtar Betara
Wani dan majalisan Borno da ya dade a zauren majalisa shi ne mai wakiltar mazabun Biu/Bayo/Shani, a 2007 Mukhtar Betara ya zo majalisa, kuma babu mamaki ya zarce har 2023. Yana daya daga cikin wadanda ake hasashen za su shugabanci majalisar idan ya zarce.

Khadijah Abba-Ibrahim
Babu macen da ta dade a majalisa kamar Khadijah Abba-Ibrahim mai wakiltar Damaturu/Gujba/Gulani/Tarmuwa, sau biyar tana cin zabe a yankinta na Jihar Yobe. A shekarar 2016, Shugaba Buhari ya nada ta ministar harkokin waje, amma a watan Janairu ta ajiye mukamin ta sake tsayawa takara ta kuma sami nasara. Ta ma taba yin takara da dan kishiyarta.
Wai shin wadannan mutane da suka dade a majalisa haka sun fi kowa cancanta ne a mazabunsu?

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Kudurin Majalisar Turai Kan Xinjiang

Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Kudurin Majalisar Turai Kan Xinjiang

LABARAI MASU NASABA

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.