ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu ‘Yan Majalisa Da Suka Shafe Shekaru Masu Yawa A Kujera

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Majalisa

Tun bayan dawowar dimokuradiyya Nijeriya a shekarar 1999, daruruwan mutane sun wakilci al’umma a mazabunsu daban-daban.

Su ‘yan majalisa ba su da ka’idar wa’adin mulki kamar yadda shugaban kasa ko gwamna ke da damar shugabanci har sau biyu ma’ana shekara 8. Hakan ya sanya wasu suke samun damar daukan shekaru masu yawan gaske a zauren majalisar tarayyar Nijeriya.

  • NNPP Ta Yi Sabbin Kamu A Jihar Kaduna

A nan ga wasu ‘yan majalisan kasa da suka kwashe sherkaru masu yawa a zauren majalisan tarayyar Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Nicholas Mutu
Tun da aka dawo mulkin farar hula a shekarar 1999, Hon. Nicholas Mutu ne yake wakiltar mutanen Bomadi/Patani na Jihar Delta a majalisar tarayya. Nicholas Mutu ya rike shugabancin kwamitin kula da hukumar bunkasa yankin Neja Delta tun daga 2009 har zuwa 2019.

Ahmad Lawan
A zaben 1999 ne Ahmad Ibrahim Lawan ya zama dan majalisar wakilai, mai wakiltar yankin Bade/Jakusko. A wannan kujera ne ya yi shekara takwas a karkashin jam’iyyar ANPP har zuwa 2007. A zaben na 2007 ne Ahmad Lawan ya zama Sanatan Arewacin Jihar Yobe. A 2019, ya karbi shugabancin majalisar dattawan Nijeriya har zuwa yau.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Femi Gbajabiamila
Femi Gbajabiamila shi ne shugaban majalisar wakilan tarayya na kasa a yau. Dan siyasan yana kan wa’adinsa na biyar kenan a kujerar majalisa. A 2003, Femi Gbajabiamila ya zama dan majalisar yankin Surulere I, tun wancan lokaci bai fadi zabe ba. Bayan shekara 16 ya zama mutum na hudu a kasar nan.

Muhammad Ali Ndume
Shi ma Muhammad Ali Ndume ya zama dan majalisar wakilai na yankin Chibok/Damboa/Gwoza ne a 2003, ya yi shekara takwas yana rike da wannan mukami. A 2011 aka zabe shi a matsayin Sanatan Kudancin Borno, har yau kuma shi ne a kan kujerar.

Ike Ekweremadu
Ba a taba yin wanda ya dade yana jagorantar majalisar dattawa kamar Sanata Ike Ekweremadu ba. Shi ma ya zo majalisa ne a 2003, kuma ya dade ana yi da shi. Ike Ekweremadu ya shafe shekaru 12 a jere a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa. Wanda shi ne ya fi dadewa a mukami a zauren majalisa.

James Manager
Ba zai yiwu a yi maganar santaocin da suka dade ba tare da an ambaci James Manager ba. Sanatan zai cika shekara 20 yana wakiltar mutanen kudancin Delta a 2023.

Leo Ogor
Wani dan siyasa da ya tare a majalisar tarayya Nijeriya tun 2003 shi ne Leo Ogor. A shekara mai zuwa dan majalisar na Isoko-North/Isoko-South zai cika shekara 20.

Alhassan Ado-Doguwa
Shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai, Alhassan Ado-Doguwa ya zo majalisa ne a 2007. Ana tunanin yana harin shugaban majalisa idan ya zarce a 2023. Shi ne dan majalisa na farko a tarihin Nijeriya wanda yana kammala bautar kasarsa aka rantsar da shi majalisa.

Mohammed Monguno
Wani wanda ya dade a majalisa kuma yana neman shugabanci shi ne Hon. Mohammed Monguno mai wakiltar Marte/Monguno/Nganzai, sau biyar ana rantsar da shi.

Kabiru Ibrahim Gaya
A shekarar 2007 ne Kabiru Ibrahim Gaya ya zama Sanatan Kudancin Kano a majalisar dattawa. Tsohon gwamnan Jihar Kano ne a jamhoriya ta uku karkashin rusasshiyar jam’iyyar NRC. A zabe mai zuwa shi ne zai sake tsaya wa jam’iyyar APC takara a Kano.

Enyinnaya Abaribe
Bayan rikicinsa da Gwamnansa a 2007, Enyinnaya Abaribe ya zama Sanatan Abiya ta Kudu a majalisa, shekararsa 15 kenan bai motsa daga majalisar dattawan ba. A 1999 shi ne mataimakin gwamnan Jihar Abiya.

Yakubu Dogara
Tsohon shugaban majaliar wakilai Yakubu Dogara yana cikin wadanda suka ga jiya da yau a majalisa, tun 2007 yake wakiltar Bogoro, Dass da Tafawa Balewa. Ya yi shugaban masu rinjaye da shugaban marasa rinjaye a zauren majalisar.

Mukhtar Betara
Wani dan majalisan Borno da ya dade a zauren majalisa shi ne mai wakiltar mazabun Biu/Bayo/Shani, a 2007 Mukhtar Betara ya zo majalisa, kuma babu mamaki ya zarce har 2023. Yana daya daga cikin wadanda ake hasashen za su shugabanci majalisar idan ya zarce.

Khadijah Abba-Ibrahim
Babu macen da ta dade a majalisa kamar Khadijah Abba-Ibrahim mai wakiltar Damaturu/Gujba/Gulani/Tarmuwa, sau biyar tana cin zabe a yankinta na Jihar Yobe. A shekarar 2016, Shugaba Buhari ya nada ta ministar harkokin waje, amma a watan Janairu ta ajiye mukamin ta sake tsayawa takara ta kuma sami nasara. Ta ma taba yin takara da dan kishiyarta.
Wai shin wadannan mutane da suka dade a majalisa haka sun fi kowa cancanta ne a mazabunsu?

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Kudurin Majalisar Turai Kan Xinjiang

Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Kudurin Majalisar Turai Kan Xinjiang

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.