ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu ‘Yan Majalisa Da Suka Shafe Shekaru Masu Yawa A Kujera

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Majalisa

Tun bayan dawowar dimokuradiyya Nijeriya a shekarar 1999, daruruwan mutane sun wakilci al’umma a mazabunsu daban-daban.

Su ‘yan majalisa ba su da ka’idar wa’adin mulki kamar yadda shugaban kasa ko gwamna ke da damar shugabanci har sau biyu ma’ana shekara 8. Hakan ya sanya wasu suke samun damar daukan shekaru masu yawan gaske a zauren majalisar tarayyar Nijeriya.

  • NNPP Ta Yi Sabbin Kamu A Jihar Kaduna

A nan ga wasu ‘yan majalisan kasa da suka kwashe sherkaru masu yawa a zauren majalisan tarayyar Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Nicholas Mutu
Tun da aka dawo mulkin farar hula a shekarar 1999, Hon. Nicholas Mutu ne yake wakiltar mutanen Bomadi/Patani na Jihar Delta a majalisar tarayya. Nicholas Mutu ya rike shugabancin kwamitin kula da hukumar bunkasa yankin Neja Delta tun daga 2009 har zuwa 2019.

Ahmad Lawan
A zaben 1999 ne Ahmad Ibrahim Lawan ya zama dan majalisar wakilai, mai wakiltar yankin Bade/Jakusko. A wannan kujera ne ya yi shekara takwas a karkashin jam’iyyar ANPP har zuwa 2007. A zaben na 2007 ne Ahmad Lawan ya zama Sanatan Arewacin Jihar Yobe. A 2019, ya karbi shugabancin majalisar dattawan Nijeriya har zuwa yau.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Femi Gbajabiamila
Femi Gbajabiamila shi ne shugaban majalisar wakilan tarayya na kasa a yau. Dan siyasan yana kan wa’adinsa na biyar kenan a kujerar majalisa. A 2003, Femi Gbajabiamila ya zama dan majalisar yankin Surulere I, tun wancan lokaci bai fadi zabe ba. Bayan shekara 16 ya zama mutum na hudu a kasar nan.

Muhammad Ali Ndume
Shi ma Muhammad Ali Ndume ya zama dan majalisar wakilai na yankin Chibok/Damboa/Gwoza ne a 2003, ya yi shekara takwas yana rike da wannan mukami. A 2011 aka zabe shi a matsayin Sanatan Kudancin Borno, har yau kuma shi ne a kan kujerar.

Ike Ekweremadu
Ba a taba yin wanda ya dade yana jagorantar majalisar dattawa kamar Sanata Ike Ekweremadu ba. Shi ma ya zo majalisa ne a 2003, kuma ya dade ana yi da shi. Ike Ekweremadu ya shafe shekaru 12 a jere a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa. Wanda shi ne ya fi dadewa a mukami a zauren majalisa.

James Manager
Ba zai yiwu a yi maganar santaocin da suka dade ba tare da an ambaci James Manager ba. Sanatan zai cika shekara 20 yana wakiltar mutanen kudancin Delta a 2023.

Leo Ogor
Wani dan siyasa da ya tare a majalisar tarayya Nijeriya tun 2003 shi ne Leo Ogor. A shekara mai zuwa dan majalisar na Isoko-North/Isoko-South zai cika shekara 20.

Alhassan Ado-Doguwa
Shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai, Alhassan Ado-Doguwa ya zo majalisa ne a 2007. Ana tunanin yana harin shugaban majalisa idan ya zarce a 2023. Shi ne dan majalisa na farko a tarihin Nijeriya wanda yana kammala bautar kasarsa aka rantsar da shi majalisa.

Mohammed Monguno
Wani wanda ya dade a majalisa kuma yana neman shugabanci shi ne Hon. Mohammed Monguno mai wakiltar Marte/Monguno/Nganzai, sau biyar ana rantsar da shi.

Kabiru Ibrahim Gaya
A shekarar 2007 ne Kabiru Ibrahim Gaya ya zama Sanatan Kudancin Kano a majalisar dattawa. Tsohon gwamnan Jihar Kano ne a jamhoriya ta uku karkashin rusasshiyar jam’iyyar NRC. A zabe mai zuwa shi ne zai sake tsaya wa jam’iyyar APC takara a Kano.

Enyinnaya Abaribe
Bayan rikicinsa da Gwamnansa a 2007, Enyinnaya Abaribe ya zama Sanatan Abiya ta Kudu a majalisa, shekararsa 15 kenan bai motsa daga majalisar dattawan ba. A 1999 shi ne mataimakin gwamnan Jihar Abiya.

Yakubu Dogara
Tsohon shugaban majaliar wakilai Yakubu Dogara yana cikin wadanda suka ga jiya da yau a majalisa, tun 2007 yake wakiltar Bogoro, Dass da Tafawa Balewa. Ya yi shugaban masu rinjaye da shugaban marasa rinjaye a zauren majalisar.

Mukhtar Betara
Wani dan majalisan Borno da ya dade a zauren majalisa shi ne mai wakiltar mazabun Biu/Bayo/Shani, a 2007 Mukhtar Betara ya zo majalisa, kuma babu mamaki ya zarce har 2023. Yana daya daga cikin wadanda ake hasashen za su shugabanci majalisar idan ya zarce.

Khadijah Abba-Ibrahim
Babu macen da ta dade a majalisa kamar Khadijah Abba-Ibrahim mai wakiltar Damaturu/Gujba/Gulani/Tarmuwa, sau biyar tana cin zabe a yankinta na Jihar Yobe. A shekarar 2016, Shugaba Buhari ya nada ta ministar harkokin waje, amma a watan Janairu ta ajiye mukamin ta sake tsayawa takara ta kuma sami nasara. Ta ma taba yin takara da dan kishiyarta.
Wai shin wadannan mutane da suka dade a majalisa haka sun fi kowa cancanta ne a mazabunsu?

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Majalisa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Kudurin Majalisar Turai Kan Xinjiang

Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Kudurin Majalisar Turai Kan Xinjiang

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.