• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Yara Da Suka Kulle Kansu A Tsohuwar Mota Sun Rasu A Neja

by Sani Anwar
1 year ago
in Labarai
0
Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gano gawawwakin wasu yara biyar a cikin wata mota da aka yasar a Minna da ke Jihar Neja, a yammacin ranar Lahadin da ta gabata.

Wannan bala’i, ya afku ne a garin Minna ta Jihar Neja; a yammacin ranar Lahadi, yayin da wasu yara su biyar suka kulle kansu a cikin wata mota na tsawon sa’o’i biyar; bisa kuskure, dukkanninsu kuma suka mutu sakamakon rashin samun damar yin numfashi.

  • An Haramta Hawan Doki Yayin Bukukuwan Sallah A Neja
  • Yadda Za Mu Fahimci Kuskuren Amurka Na Cewa Wai Kasar Sin “Ta Wuce Gona Da Iri” Wajen Samar Da Hajoji

Wannan iftila’i da ya faru a garin Gurara Albishir da ke kan titin Bidda na garin Minna, ya yi matukar jefa al’ummar wannan gari cikin alhini.

Binciken Jaridar LEADERSHIP ya gano cewa, yaran suna yin wasa ne a wani katafaren gida da ke kusa da gidansu, inda suka kulle kansu bisa kuskure a cikin wata mota kirar Honda da aka jima da yin watsi da ita har tsawon shekaru biyu.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa, tun misalin karfe 11:00 na safe ne; wadannan yara suka kulle kansu, yayin da kuma iyayensu ke can suna ta faman neman su; ba su gan su ba, har sai lokacin da aka gano gawarwakinsu a cikin wannan mota da misalin karfe 4:00 na yamma.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

Har ila yau, rahoton ya bayyana cewa; wadanda wannan iftila’i ya rutsa da su, hudu mata ne da kuma namiji daya; sannan uku daga cikinsu ‘yan’uwan juna ne, wadanda su kenan iyayensu suka haifa a duniya. Sauran biyun kuma da suka mutu, iyayensu daban-daban ne; ciki har da shi kansa mai motar.

Haka zalika, an bayyana sunan wadannan yara da shekarunsu kamar haka: Zahra ‘yar shekara 10, Aisha mai shekaru 7, Fati ‘yar shekara 5 da kuma Isah dan shekara 7, duk dai da cewa LEADERSHIP ta kasa tantance ko wane ne cikon na 5 din.

Shugaban Karamar Hukumar Chanchaga, Aminu Ladan; wanda gidansa ke kusa da unguwar da wannan al’amari ya faru, ya ziyarci wajen ba tare da wani bata lokaci ba.

Kazalika, ya tabbatar wa da manema labarai faruwar wannan al’amari tare da bayyana iftila’in a matsayin wani babban abin takaici, sannan kuma a karshe ya jajanta wa iyayen wadannan yara da suka rasu.

Bugu da kari, har zuwa lokacin hada wannan rahoto; ba mu samu damar jin ta bakin Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yansanda (PPRO), Wasiu Abiodun ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wuraren Bayar Da Tallafi Sun Zama Tarkon Mutuwa

Next Post

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (6)

Related

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

7 hours ago
'yansanda
Labarai

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai
Labarai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

9 hours ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

11 hours ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

12 hours ago
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

14 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (6)

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
neja

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.