• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Yara Da Suka Kulle Kansu A Tsohuwar Mota Sun Rasu A Neja

by Sani Anwar
1 year ago
in Labarai
0
Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gano gawawwakin wasu yara biyar a cikin wata mota da aka yasar a Minna da ke Jihar Neja, a yammacin ranar Lahadin da ta gabata.

Wannan bala’i, ya afku ne a garin Minna ta Jihar Neja; a yammacin ranar Lahadi, yayin da wasu yara su biyar suka kulle kansu a cikin wata mota na tsawon sa’o’i biyar; bisa kuskure, dukkanninsu kuma suka mutu sakamakon rashin samun damar yin numfashi.

  • An Haramta Hawan Doki Yayin Bukukuwan Sallah A Neja
  • Yadda Za Mu Fahimci Kuskuren Amurka Na Cewa Wai Kasar Sin “Ta Wuce Gona Da Iri” Wajen Samar Da Hajoji

Wannan iftila’i da ya faru a garin Gurara Albishir da ke kan titin Bidda na garin Minna, ya yi matukar jefa al’ummar wannan gari cikin alhini.

Binciken Jaridar LEADERSHIP ya gano cewa, yaran suna yin wasa ne a wani katafaren gida da ke kusa da gidansu, inda suka kulle kansu bisa kuskure a cikin wata mota kirar Honda da aka jima da yin watsi da ita har tsawon shekaru biyu.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa, tun misalin karfe 11:00 na safe ne; wadannan yara suka kulle kansu, yayin da kuma iyayensu ke can suna ta faman neman su; ba su gan su ba, har sai lokacin da aka gano gawarwakinsu a cikin wannan mota da misalin karfe 4:00 na yamma.

Labarai Masu Nasaba

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Har ila yau, rahoton ya bayyana cewa; wadanda wannan iftila’i ya rutsa da su, hudu mata ne da kuma namiji daya; sannan uku daga cikinsu ‘yan’uwan juna ne, wadanda su kenan iyayensu suka haifa a duniya. Sauran biyun kuma da suka mutu, iyayensu daban-daban ne; ciki har da shi kansa mai motar.

Haka zalika, an bayyana sunan wadannan yara da shekarunsu kamar haka: Zahra ‘yar shekara 10, Aisha mai shekaru 7, Fati ‘yar shekara 5 da kuma Isah dan shekara 7, duk dai da cewa LEADERSHIP ta kasa tantance ko wane ne cikon na 5 din.

Shugaban Karamar Hukumar Chanchaga, Aminu Ladan; wanda gidansa ke kusa da unguwar da wannan al’amari ya faru, ya ziyarci wajen ba tare da wani bata lokaci ba.

Kazalika, ya tabbatar wa da manema labarai faruwar wannan al’amari tare da bayyana iftila’in a matsayin wani babban abin takaici, sannan kuma a karshe ya jajanta wa iyayen wadannan yara da suka rasu.

Bugu da kari, har zuwa lokacin hada wannan rahoto; ba mu samu damar jin ta bakin Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yansanda (PPRO), Wasiu Abiodun ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wuraren Bayar Da Tallafi Sun Zama Tarkon Mutuwa

Next Post

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (6)

Related

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

3 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

15 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

16 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (6)

LABARAI MASU NASABA

Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.