• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Yara Da Suka Kulle Kansu A Tsohuwar Mota Sun Rasu A Neja

by Sani Anwar
1 year ago
in Labarai
0
Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gano gawawwakin wasu yara biyar a cikin wata mota da aka yasar a Minna da ke Jihar Neja, a yammacin ranar Lahadin da ta gabata.

Wannan bala’i, ya afku ne a garin Minna ta Jihar Neja; a yammacin ranar Lahadi, yayin da wasu yara su biyar suka kulle kansu a cikin wata mota na tsawon sa’o’i biyar; bisa kuskure, dukkanninsu kuma suka mutu sakamakon rashin samun damar yin numfashi.

  • An Haramta Hawan Doki Yayin Bukukuwan Sallah A Neja
  • Yadda Za Mu Fahimci Kuskuren Amurka Na Cewa Wai Kasar Sin “Ta Wuce Gona Da Iri” Wajen Samar Da Hajoji

Wannan iftila’i da ya faru a garin Gurara Albishir da ke kan titin Bidda na garin Minna, ya yi matukar jefa al’ummar wannan gari cikin alhini.

Binciken Jaridar LEADERSHIP ya gano cewa, yaran suna yin wasa ne a wani katafaren gida da ke kusa da gidansu, inda suka kulle kansu bisa kuskure a cikin wata mota kirar Honda da aka jima da yin watsi da ita har tsawon shekaru biyu.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa, tun misalin karfe 11:00 na safe ne; wadannan yara suka kulle kansu, yayin da kuma iyayensu ke can suna ta faman neman su; ba su gan su ba, har sai lokacin da aka gano gawarwakinsu a cikin wannan mota da misalin karfe 4:00 na yamma.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Har ila yau, rahoton ya bayyana cewa; wadanda wannan iftila’i ya rutsa da su, hudu mata ne da kuma namiji daya; sannan uku daga cikinsu ‘yan’uwan juna ne, wadanda su kenan iyayensu suka haifa a duniya. Sauran biyun kuma da suka mutu, iyayensu daban-daban ne; ciki har da shi kansa mai motar.

Haka zalika, an bayyana sunan wadannan yara da shekarunsu kamar haka: Zahra ‘yar shekara 10, Aisha mai shekaru 7, Fati ‘yar shekara 5 da kuma Isah dan shekara 7, duk dai da cewa LEADERSHIP ta kasa tantance ko wane ne cikon na 5 din.

Shugaban Karamar Hukumar Chanchaga, Aminu Ladan; wanda gidansa ke kusa da unguwar da wannan al’amari ya faru, ya ziyarci wajen ba tare da wani bata lokaci ba.

Kazalika, ya tabbatar wa da manema labarai faruwar wannan al’amari tare da bayyana iftila’in a matsayin wani babban abin takaici, sannan kuma a karshe ya jajanta wa iyayen wadannan yara da suka rasu.

Bugu da kari, har zuwa lokacin hada wannan rahoto; ba mu samu damar jin ta bakin Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yansanda (PPRO), Wasiu Abiodun ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wuraren Bayar Da Tallafi Sun Zama Tarkon Mutuwa

Next Post

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (6)

Related

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

8 hours ago
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
Labarai

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

8 hours ago
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
Tsaro

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

11 hours ago
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
Manyan Labarai

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

12 hours ago
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

13 hours ago
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

14 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Girman Darajar Manzon Allah (SAW) Da Allah Ya Yi Rantsuwa Da Ita (6)

LABARAI MASU NASABA

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.