• English
  • Business News
Monday, May 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Kungiya Ta Wayar Da Kan Mutane Kan Dokar Cin Zarafin Jinsi A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Wata Kungiya Ta Wayar Da Kan Mutane Kan Dokar Cin Zarafin Jinsi A Jihar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai zaman kanta, Women Voice and Leadership Project (WVL) ta wayar da kan masu ruwa da tsaki a kan aiwatar da dokar cin zarafin jinsi (GBV) a Kebbi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Global Affairs Canada ce ke daukar nauyin shirin na WVL da ActionAid Nijeriya ke gudanarwa.

  • Auren Gata : Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Aurar Da Mata 300
  • Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Tabbatar Da Nasir Idris A Matsayin Gwamnan Jihar Kebbi

Ya kuma bayar da rahoton cewa, wayar da kan jama’a ya kunshi taron tattaunawa kan aiwatar da dokar hana cin zarafin bil’adama (VAPP) a Kebbi.

Da take zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron tattaunawa da aka yi a Birnin Kebbi, Babbar Daraktar kungiyar ta Nana, Dakta Fatima Adamu ta ce sun hada kungiyoyi daban-daban na al’umma.

“Mun tattaro kungiyoyi daban-daban na al’umma kuma mun kira kanmu Collision of Community-based Organizations (CBOs) Against Henders Colence a Kebbi.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

Dokta Fatima Adamu ta ce, “Babban makasudin haduwa don tattaunawar ita ce tattaunawa mai ma’ana a tsakanin masu ruwa da tsaki don aiwatar da dokar cin zarafin jinsi musammam irin yadda ake yiwa ‘ya’ya mata fyade da cin zarafi a gidajen aure ko a waje.

Ta kara da cewa tattaunawar ta kasance kan matakin aiwatarwa, nasarori da kalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da dokar VAPP a jihar Kebbi, inda ta ce tattaunawar ta hada jami’an gwamnati, kungiyoyin farar hula, masana shari’a da shugabannin al’umma.

A cewarta, da nufin samar da wani dandali ga masu ruwa da tsaki domin yin musayar ra’ayi, tattauna hanyoyin da suka dace da kuma magance kalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da dokar VAPP a jihar baki daya.

Shugabar ta tuna cewa kimanin shekaru biyu da suka gabata sun ba da shawarar kuma sun sami amincewa da Dokar VAPP, tana mai cewa: “amma mun lura cewa an yi shiru, mun gano inda muke da kalubalen da muke fuskanta don samar da mafita.

“Kawai masu ruwa da tsaki wadanda ke da rawar da za su taka wajen aiwatar da shirin da aka gayyata kuma duk mun amince cewa wannan mafari ne, wasu sun ba da shawarar a rika shirya shi duk shekara ko shekara biyu domin a nuna inda muke wajen aiwatar da shi. ” in ji ta.

Dangane da kalubalantar katsalandan a shari’ar VAPP da wasu manyan ‘yan siyasa da wasu masu hannu da shuni ke yi a cikin al’umma, Daraktar ta ce wasu daga cikin wadannan mutane sun kai ga baiwa jami’an shari’a da jami’an tsaro cin hanci don samun mafita ga shari’un fyade ko na cin zarafin jinsi.

Hakazalika ta koka da yadda wasu daga cikin irin wadannan mutane kan yi amfani da karfinsu wajen biyan iyayen wadanda suka tsira da ransu wajen lalata shari’ar, yayin da wasu ke yin tasiri ga umurnin da aka bayar na a lalata shari’ar a yayin da ta ke a gaban alkalai.

Duk da haka, Dakta Fatima Adamu ta ce sun fahimci cewa a cikin dokar, “akwai dokar kariya da ya kamata ta magance irin wannan yanayin amma ba mu yi amfani da shi ba. Don haka, yanzu muna da kalubalen don ganin yadda za mu iya jajircewa wajen amfani dokar, inji ta.”

Haka kuma ta kara da bayar da shawarar shigar da kafafen yada labarai a cikin shari’o’in da ke da karfin gaske da nufin yada lamarin don hana ci gaba da lalata shari’o’in a yayin da suke a gaban kotu daga manyan mutane da masu fada a ji.

Daga karshe ta ce ina sa ran kungiyar sa kai a karshen shirin gaba dayan shi, zasu jajirce wajen ganin an rage da hana yawan kararraki ta hanyar karya al’adar yin shiru da tsoma baki daga masu iko da masu arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DokaJinsiKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaɓen Cike-gurbi: PDP Ta Lashe Zaɓen Ɗan Majalisar Jiha A Mazaɓar Mayo-Belwa A Adamawa

Next Post

An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

Related

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

2 hours ago
Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe
Labarai

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

13 hours ago
An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja
Labarai

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

14 hours ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
Labarai

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana

18 hours ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)
Labarai

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (I)

20 hours ago
Kano
Labarai

Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta

20 hours ago
Next Post
An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

LABARAI MASU NASABA

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

May 19, 2025
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

May 19, 2025
Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

May 18, 2025
Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

May 18, 2025
Ciwon Mara Lokacin Al’ada

Ciwon Mara Lokacin Al’ada

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

May 18, 2025
Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

May 18, 2025
An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

May 18, 2025
Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

May 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.