• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Kungiya Ta Wayar Da Kan Mutane Kan Dokar Cin Zarafin Jinsi A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Wata Kungiya Ta Wayar Da Kan Mutane Kan Dokar Cin Zarafin Jinsi A Jihar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai zaman kanta, Women Voice and Leadership Project (WVL) ta wayar da kan masu ruwa da tsaki a kan aiwatar da dokar cin zarafin jinsi (GBV) a Kebbi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Global Affairs Canada ce ke daukar nauyin shirin na WVL da ActionAid Nijeriya ke gudanarwa.

  • Auren Gata : Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Aurar Da Mata 300
  • Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Tabbatar Da Nasir Idris A Matsayin Gwamnan Jihar Kebbi

Ya kuma bayar da rahoton cewa, wayar da kan jama’a ya kunshi taron tattaunawa kan aiwatar da dokar hana cin zarafin bil’adama (VAPP) a Kebbi.

Da take zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron tattaunawa da aka yi a Birnin Kebbi, Babbar Daraktar kungiyar ta Nana, Dakta Fatima Adamu ta ce sun hada kungiyoyi daban-daban na al’umma.

“Mun tattaro kungiyoyi daban-daban na al’umma kuma mun kira kanmu Collision of Community-based Organizations (CBOs) Against Henders Colence a Kebbi.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Dokta Fatima Adamu ta ce, “Babban makasudin haduwa don tattaunawar ita ce tattaunawa mai ma’ana a tsakanin masu ruwa da tsaki don aiwatar da dokar cin zarafin jinsi musammam irin yadda ake yiwa ‘ya’ya mata fyade da cin zarafi a gidajen aure ko a waje.

Ta kara da cewa tattaunawar ta kasance kan matakin aiwatarwa, nasarori da kalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da dokar VAPP a jihar Kebbi, inda ta ce tattaunawar ta hada jami’an gwamnati, kungiyoyin farar hula, masana shari’a da shugabannin al’umma.

A cewarta, da nufin samar da wani dandali ga masu ruwa da tsaki domin yin musayar ra’ayi, tattauna hanyoyin da suka dace da kuma magance kalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da dokar VAPP a jihar baki daya.

Shugabar ta tuna cewa kimanin shekaru biyu da suka gabata sun ba da shawarar kuma sun sami amincewa da Dokar VAPP, tana mai cewa: “amma mun lura cewa an yi shiru, mun gano inda muke da kalubalen da muke fuskanta don samar da mafita.

“Kawai masu ruwa da tsaki wadanda ke da rawar da za su taka wajen aiwatar da shirin da aka gayyata kuma duk mun amince cewa wannan mafari ne, wasu sun ba da shawarar a rika shirya shi duk shekara ko shekara biyu domin a nuna inda muke wajen aiwatar da shi. ” in ji ta.

Dangane da kalubalantar katsalandan a shari’ar VAPP da wasu manyan ‘yan siyasa da wasu masu hannu da shuni ke yi a cikin al’umma, Daraktar ta ce wasu daga cikin wadannan mutane sun kai ga baiwa jami’an shari’a da jami’an tsaro cin hanci don samun mafita ga shari’un fyade ko na cin zarafin jinsi.

Hakazalika ta koka da yadda wasu daga cikin irin wadannan mutane kan yi amfani da karfinsu wajen biyan iyayen wadanda suka tsira da ransu wajen lalata shari’ar, yayin da wasu ke yin tasiri ga umurnin da aka bayar na a lalata shari’ar a yayin da ta ke a gaban alkalai.

Duk da haka, Dakta Fatima Adamu ta ce sun fahimci cewa a cikin dokar, “akwai dokar kariya da ya kamata ta magance irin wannan yanayin amma ba mu yi amfani da shi ba. Don haka, yanzu muna da kalubalen don ganin yadda za mu iya jajircewa wajen amfani dokar, inji ta.”

Haka kuma ta kara da bayar da shawarar shigar da kafafen yada labarai a cikin shari’o’in da ke da karfin gaske da nufin yada lamarin don hana ci gaba da lalata shari’o’in a yayin da suke a gaban kotu daga manyan mutane da masu fada a ji.

Daga karshe ta ce ina sa ran kungiyar sa kai a karshen shirin gaba dayan shi, zasu jajirce wajen ganin an rage da hana yawan kararraki ta hanyar karya al’adar yin shiru da tsoma baki daga masu iko da masu arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DokaJinsiKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaɓen Cike-gurbi: PDP Ta Lashe Zaɓen Ɗan Majalisar Jiha A Mazaɓar Mayo-Belwa A Adamawa

Next Post

An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

3 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

6 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

8 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

11 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

12 hours ago
Next Post
An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.