ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Kungiya Ta Wayar Da Kan Mutane Kan Dokar Cin Zarafin Jinsi A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Kebbi

Wata kungiya mai zaman kanta, Women Voice and Leadership Project (WVL) ta wayar da kan masu ruwa da tsaki a kan aiwatar da dokar cin zarafin jinsi (GBV) a Kebbi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Global Affairs Canada ce ke daukar nauyin shirin na WVL da ActionAid Nijeriya ke gudanarwa.

  • Auren Gata : Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Aurar Da Mata 300
  • Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Tabbatar Da Nasir Idris A Matsayin Gwamnan Jihar Kebbi

Ya kuma bayar da rahoton cewa, wayar da kan jama’a ya kunshi taron tattaunawa kan aiwatar da dokar hana cin zarafin bil’adama (VAPP) a Kebbi.

ADVERTISEMENT

Da take zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron tattaunawa da aka yi a Birnin Kebbi, Babbar Daraktar kungiyar ta Nana, Dakta Fatima Adamu ta ce sun hada kungiyoyi daban-daban na al’umma.

“Mun tattaro kungiyoyi daban-daban na al’umma kuma mun kira kanmu Collision of Community-based Organizations (CBOs) Against Henders Colence a Kebbi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dokta Fatima Adamu ta ce, “Babban makasudin haduwa don tattaunawar ita ce tattaunawa mai ma’ana a tsakanin masu ruwa da tsaki don aiwatar da dokar cin zarafin jinsi musammam irin yadda ake yiwa ‘ya’ya mata fyade da cin zarafi a gidajen aure ko a waje.

Ta kara da cewa tattaunawar ta kasance kan matakin aiwatarwa, nasarori da kalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da dokar VAPP a jihar Kebbi, inda ta ce tattaunawar ta hada jami’an gwamnati, kungiyoyin farar hula, masana shari’a da shugabannin al’umma.

A cewarta, da nufin samar da wani dandali ga masu ruwa da tsaki domin yin musayar ra’ayi, tattauna hanyoyin da suka dace da kuma magance kalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da dokar VAPP a jihar baki daya.

Shugabar ta tuna cewa kimanin shekaru biyu da suka gabata sun ba da shawarar kuma sun sami amincewa da Dokar VAPP, tana mai cewa: “amma mun lura cewa an yi shiru, mun gano inda muke da kalubalen da muke fuskanta don samar da mafita.

“Kawai masu ruwa da tsaki wadanda ke da rawar da za su taka wajen aiwatar da shirin da aka gayyata kuma duk mun amince cewa wannan mafari ne, wasu sun ba da shawarar a rika shirya shi duk shekara ko shekara biyu domin a nuna inda muke wajen aiwatar da shi. ” in ji ta.

Dangane da kalubalantar katsalandan a shari’ar VAPP da wasu manyan ‘yan siyasa da wasu masu hannu da shuni ke yi a cikin al’umma, Daraktar ta ce wasu daga cikin wadannan mutane sun kai ga baiwa jami’an shari’a da jami’an tsaro cin hanci don samun mafita ga shari’un fyade ko na cin zarafin jinsi.

Hakazalika ta koka da yadda wasu daga cikin irin wadannan mutane kan yi amfani da karfinsu wajen biyan iyayen wadanda suka tsira da ransu wajen lalata shari’ar, yayin da wasu ke yin tasiri ga umurnin da aka bayar na a lalata shari’ar a yayin da ta ke a gaban alkalai.

Duk da haka, Dakta Fatima Adamu ta ce sun fahimci cewa a cikin dokar, “akwai dokar kariya da ya kamata ta magance irin wannan yanayin amma ba mu yi amfani da shi ba. Don haka, yanzu muna da kalubalen don ganin yadda za mu iya jajircewa wajen amfani dokar, inji ta.”

Haka kuma ta kara da bayar da shawarar shigar da kafafen yada labarai a cikin shari’o’in da ke da karfin gaske da nufin yada lamarin don hana ci gaba da lalata shari’o’in a yayin da suke a gaban kotu daga manyan mutane da masu fada a ji.

Daga karshe ta ce ina sa ran kungiyar sa kai a karshen shirin gaba dayan shi, zasu jajirce wajen ganin an rage da hana yawan kararraki ta hanyar karya al’adar yin shiru da tsoma baki daga masu iko da masu arziki.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.