ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Kungiya Ta Wayar Da Kan Mutane Kan Dokar Cin Zarafin Jinsi A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Kebbi

Wata kungiya mai zaman kanta, Women Voice and Leadership Project (WVL) ta wayar da kan masu ruwa da tsaki a kan aiwatar da dokar cin zarafin jinsi (GBV) a Kebbi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Global Affairs Canada ce ke daukar nauyin shirin na WVL da ActionAid Nijeriya ke gudanarwa.

  • Auren Gata : Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Aurar Da Mata 300
  • Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Tabbatar Da Nasir Idris A Matsayin Gwamnan Jihar Kebbi

Ya kuma bayar da rahoton cewa, wayar da kan jama’a ya kunshi taron tattaunawa kan aiwatar da dokar hana cin zarafin bil’adama (VAPP) a Kebbi.

ADVERTISEMENT

Da take zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron tattaunawa da aka yi a Birnin Kebbi, Babbar Daraktar kungiyar ta Nana, Dakta Fatima Adamu ta ce sun hada kungiyoyi daban-daban na al’umma.

“Mun tattaro kungiyoyi daban-daban na al’umma kuma mun kira kanmu Collision of Community-based Organizations (CBOs) Against Henders Colence a Kebbi.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Dokta Fatima Adamu ta ce, “Babban makasudin haduwa don tattaunawar ita ce tattaunawa mai ma’ana a tsakanin masu ruwa da tsaki don aiwatar da dokar cin zarafin jinsi musammam irin yadda ake yiwa ‘ya’ya mata fyade da cin zarafi a gidajen aure ko a waje.

Ta kara da cewa tattaunawar ta kasance kan matakin aiwatarwa, nasarori da kalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da dokar VAPP a jihar Kebbi, inda ta ce tattaunawar ta hada jami’an gwamnati, kungiyoyin farar hula, masana shari’a da shugabannin al’umma.

A cewarta, da nufin samar da wani dandali ga masu ruwa da tsaki domin yin musayar ra’ayi, tattauna hanyoyin da suka dace da kuma magance kalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da dokar VAPP a jihar baki daya.

Shugabar ta tuna cewa kimanin shekaru biyu da suka gabata sun ba da shawarar kuma sun sami amincewa da Dokar VAPP, tana mai cewa: “amma mun lura cewa an yi shiru, mun gano inda muke da kalubalen da muke fuskanta don samar da mafita.

“Kawai masu ruwa da tsaki wadanda ke da rawar da za su taka wajen aiwatar da shirin da aka gayyata kuma duk mun amince cewa wannan mafari ne, wasu sun ba da shawarar a rika shirya shi duk shekara ko shekara biyu domin a nuna inda muke wajen aiwatar da shi. ” in ji ta.

Dangane da kalubalantar katsalandan a shari’ar VAPP da wasu manyan ‘yan siyasa da wasu masu hannu da shuni ke yi a cikin al’umma, Daraktar ta ce wasu daga cikin wadannan mutane sun kai ga baiwa jami’an shari’a da jami’an tsaro cin hanci don samun mafita ga shari’un fyade ko na cin zarafin jinsi.

Hakazalika ta koka da yadda wasu daga cikin irin wadannan mutane kan yi amfani da karfinsu wajen biyan iyayen wadanda suka tsira da ransu wajen lalata shari’ar, yayin da wasu ke yin tasiri ga umurnin da aka bayar na a lalata shari’ar a yayin da ta ke a gaban alkalai.

Duk da haka, Dakta Fatima Adamu ta ce sun fahimci cewa a cikin dokar, “akwai dokar kariya da ya kamata ta magance irin wannan yanayin amma ba mu yi amfani da shi ba. Don haka, yanzu muna da kalubalen don ganin yadda za mu iya jajircewa wajen amfani dokar, inji ta.”

Haka kuma ta kara da bayar da shawarar shigar da kafafen yada labarai a cikin shari’o’in da ke da karfin gaske da nufin yada lamarin don hana ci gaba da lalata shari’o’in a yayin da suke a gaban kotu daga manyan mutane da masu fada a ji.

Daga karshe ta ce ina sa ran kungiyar sa kai a karshen shirin gaba dayan shi, zasu jajirce wajen ganin an rage da hana yawan kararraki ta hanyar karya al’adar yin shiru da tsoma baki daga masu iko da masu arziki.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

An Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Ƙarshen Ƙalubalen Rashin Wutar Lantarki A Jere

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.