Abba Ibrahim Wada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Watakila Zidane Ya Koma Juventus

by Abba Ibrahim Wada
December 20, 2020
in WASANNI
2 min read
Real Madrid Za Ta Kashe Fam Miliyan 460 Wajen Sayan Manyan ‘Yan Wasa

File photo dated 26-05-2018 of Zinedine Zidane.

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wasu rahotanni daga kasar Italiya sun ruwaito cewa watakila tsohon dan wasan tawagar kasar Faransa, Zinadine Zidane, ya koma koyar da kungiyar Juventus da koyarwa, idan har ya bar kungiyar Real Madrid a karshen kakar wasa ta bana.
A kwanakin baya ne Zinedine Zidane, wanda ya taba bugawa Juventus wasa a shekarun baya ya bayyana cewa ya shirya tsaf domin yin hannun riga da Real Madrid a karshen wannan kaka da muke ciki duba da yadda yake ganin yanayin al’amura a kungiyar babu tabbas.
Rahotanni dai na cewa Zidane ya bukaci hukumomin kungiyar su sayo mai ‘yan wasa da suka hada da Paul Pogba na Manchester United da Sadio Mane na Liberpool da Eduardo Camabinga, amma maimakon haka suka bar shi da ‘yan wasan da ba sa iya rawar gaban hantsi.
Mujallar Dariogol da ake wallafawa a kasar Spain ta ruwaito cewa Zidane zai yi hannun riga da Bernabeu a karshen wannan kaka a matsayin sakamakon tattaunawar fahimtar juna da suka yi da shugaban gudanarwar kungiyar.
Sai dai wasu rahotanni kuma sun bayyana cewa shugaban gudanarwar kungiyar Florentino Perez ya yiwa Zidane alwashin cewa a karshen kakar wasa kungiyar zata saki kudade domin sayan ‘yan wasan da zasu karawa kungiyar karfi.
Sai dai babu tabbas idan kungiyar zata iya sayan ‘yan wasan da Zidane yake fatan yin aiki dasu duba da irin halin matsin tattalin arzikin da duniya ta shiga sakamakon annobar cutar Korona wadda ta talauta kungiyoyi kuma hakan yasa ake ganin zai iya komawa tsohuwar kungiyar daya bugawa kwallo a baya domin ya koyar da ita.
Kawo yanzu dai Andre Pirlo shi ne yake koyar da kungiyar Juventus amma duk da haka kungiyar bata buga wasa kamar na kakar data gabata kuma kungiyar tana mataki na uku akan teburin Siriya A bugu da kari canjaras shida kungiyar ta buga a wannan kakar.
A kakar wasa mai zuwa Juventus zata fitar da kudi domin sayan manyan ‘yan wasa ciki har da Paul Pogba da Kylian Mbappe wanda hakan yasa ake ganin Zidane zai koma Juventus din da koyarwa

SendShareTweetShare
Previous Post

Bai Kamata A Tuhumi Cavani Ba

Next Post

Ozil Zai Fara Buga Wasa A Arsenal A Watan Janairu

RelatedPosts

La Liga

Yau Za A Cigaba Da Buga Wasannin Laliga

by Abba Ibrahim Wada
10 hours ago
0

A yau Talata za a ci gaba da buga wasannin...

Benzema

Shin Ya Kamata Real Madrid Ta Dogara Da Benzema Wajen Cin Kwallaye?

by Abba Ibrahim Wada
10 hours ago
0

Sau da dama kociyan kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid,...

Diego Costa

Wace Kungiya Ce  Zata Dauki Diego Costa

by Abba Ibrahim Wada
1 day ago
0

Tun bayan da kungiyar kwallon kafa ta Atletico Madrid, ta...

Next Post
Ozil Zai Fara Buga Wasa A Arsenal A Watan Janairu

Ozil Zai Fara Buga Wasa A Arsenal A Watan Janairu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version