ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Watsi Da Tarihi Cin Amana Ne

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 days ago
Tarihi

A ranar 13 ga watan Disamban shekarar 1937, dan kasar Jamus John Rabe, ya rubuta cikin kundin adana bayanansa cewa, “an sake jefa boma-bomai masu dimbin yawa, sa’an nan, a kan hanyarmu ta zuwa titin Shanghai, ko ina ana iya ganin gawawwakin fararen hula. A gabanmu, mun ga dakarun mamaya na kasar Japan.”

Cikin kundin, John Rabe ya rubuta ta’asar da sojojin Japan suka aikata a birnin Nanjing na kasar Sin, a ranar 13 ga watan Disamban shekarar ta 1937, hakan ya sa kundin ya kasance muhimmiyar shaida, da ta fayyace gaskiyar kisan kiyashin birnin Nanjing.

Dakarun mamaya na kasar Japan sun hallaka Sinawa 300,000, tare da cin zarafin mata masu dimbin yawa. Kazalika yara da yawa sun rasa rayukansu, kuma an rusa kaso 1 bisa 3 na daukacin gidajen birnin, tare da kwashe dukiyoyi masu dumbin yawa. Kisan kiyashin birnin Nanjing da dakarun mamaya na kasar Japan suka aikata, ya zama laifin cin zarafin dan Adam, kuma babu wanda zai iya musanta wannan lamari, ganin yadda aka tattara shaidu masu karfi dake tabbatar da aukuwarsa.

ADVERTISEMENT

To sai dai kuma ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar Japan ta ki amincewa da kuskuren da ta aikata na tayar da yaki, maimakon hakan ma, ana iya ganin masu aikata laifuffukan tayar da yakin suna dawowa teburin siyasar Japan, kana shugabanni, da manyan jami’an kasar da dama suna kai ziyara haikalin Yasukuni, inda suke girmama kaburburan mayakan da suka jagorancin aikata wancan ta’asa.

A farkon watan Nuwamban bana, firaministar kasar Japan Takaichi Sanae ta bayyana cewa, matsalar Taiwan tana da alaka da tsaron kasar Japan, inda ta nuna cewa, mai iyuwa ne kasar Japan ta dauki matakan soja, wajen tsoma hannu cikin harkokin Taiwan na kasar Sin. Wannan tsokacin da ta yi, ya yi kama da tsohuwar dabi’ar kasar Japan ta amfani da karfin soji.

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

Watsi da tarihi cin amana ne kana kin amincewa da aikata laifi tamkar sake aikawa ne. A bana, ake cika shekaru 80 da Sinawa suka samu nasara a yaki da maharan Japan da ma yakin duniya na II, kuma ba zai yiwu a musanta kisan kiyashin birnin Nanjing ba. Abubuwan da Takaichi Sanae, da ma sauran ‘yan siyasa da dama na kasar Japan suka aikata na musantawa da kokarin gyara tarihi, sun kasance laifi na farfado da dabi’ar Japan ta amfani da karfin soji, lamarin da ya illata dokar kasa da kasa, tare da gurgunta nasarar da aka cimma a yakin duniya na biyu, kana ya bakanta ran gamayyar kasa da kasa. Tabbas, tarihi zai wanzar da cewa, adalci, da haske, da kuma ci gaba, za su yi galaba kan yaki da rashin adalci, da duhu, da kuma tashe-tashen hankula! (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow
Daga Birnin Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Gwamnan Kano Ya Kafa Sabuwar Rundunar Tsaron Tashoshin Mota

Gwamnan Kano Ya Kafa Sabuwar Rundunar Tsaron Tashoshin Mota

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.