ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Watsi Da Tarihi Cin Amana Ne

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Tarihi

A ranar 13 ga watan Disamban shekarar 1937, dan kasar Jamus John Rabe, ya rubuta cikin kundin adana bayanansa cewa, “an sake jefa boma-bomai masu dimbin yawa, sa’an nan, a kan hanyarmu ta zuwa titin Shanghai, ko ina ana iya ganin gawawwakin fararen hula. A gabanmu, mun ga dakarun mamaya na kasar Japan.”

Cikin kundin, John Rabe ya rubuta ta’asar da sojojin Japan suka aikata a birnin Nanjing na kasar Sin, a ranar 13 ga watan Disamban shekarar ta 1937, hakan ya sa kundin ya kasance muhimmiyar shaida, da ta fayyace gaskiyar kisan kiyashin birnin Nanjing.

Dakarun mamaya na kasar Japan sun hallaka Sinawa 300,000, tare da cin zarafin mata masu dimbin yawa. Kazalika yara da yawa sun rasa rayukansu, kuma an rusa kaso 1 bisa 3 na daukacin gidajen birnin, tare da kwashe dukiyoyi masu dumbin yawa. Kisan kiyashin birnin Nanjing da dakarun mamaya na kasar Japan suka aikata, ya zama laifin cin zarafin dan Adam, kuma babu wanda zai iya musanta wannan lamari, ganin yadda aka tattara shaidu masu karfi dake tabbatar da aukuwarsa.

ADVERTISEMENT

To sai dai kuma ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar Japan ta ki amincewa da kuskuren da ta aikata na tayar da yaki, maimakon hakan ma, ana iya ganin masu aikata laifuffukan tayar da yakin suna dawowa teburin siyasar Japan, kana shugabanni, da manyan jami’an kasar da dama suna kai ziyara haikalin Yasukuni, inda suke girmama kaburburan mayakan da suka jagorancin aikata wancan ta’asa.

A farkon watan Nuwamban bana, firaministar kasar Japan Takaichi Sanae ta bayyana cewa, matsalar Taiwan tana da alaka da tsaron kasar Japan, inda ta nuna cewa, mai iyuwa ne kasar Japan ta dauki matakan soja, wajen tsoma hannu cikin harkokin Taiwan na kasar Sin. Wannan tsokacin da ta yi, ya yi kama da tsohuwar dabi’ar kasar Japan ta amfani da karfin soji.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Watsi da tarihi cin amana ne kana kin amincewa da aikata laifi tamkar sake aikawa ne. A bana, ake cika shekaru 80 da Sinawa suka samu nasara a yaki da maharan Japan da ma yakin duniya na II, kuma ba zai yiwu a musanta kisan kiyashin birnin Nanjing ba. Abubuwan da Takaichi Sanae, da ma sauran ‘yan siyasa da dama na kasar Japan suka aikata na musantawa da kokarin gyara tarihi, sun kasance laifi na farfado da dabi’ar Japan ta amfani da karfin soji, lamarin da ya illata dokar kasa da kasa, tare da gurgunta nasarar da aka cimma a yakin duniya na biyu, kana ya bakanta ran gamayyar kasa da kasa. Tabbas, tarihi zai wanzar da cewa, adalci, da haske, da kuma ci gaba, za su yi galaba kan yaki da rashin adalci, da duhu, da kuma tashe-tashen hankula! (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

Tarihi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
Tarihi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Kafa Sabuwar Rundunar Tsaron Tashoshin Mota

Gwamnan Kano Ya Kafa Sabuwar Rundunar Tsaron Tashoshin Mota

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.