ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Watsi Da Tarihi Cin Amana Ne

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Tarihi

A ranar 13 ga watan Disamban shekarar 1937, dan kasar Jamus John Rabe, ya rubuta cikin kundin adana bayanansa cewa, “an sake jefa boma-bomai masu dimbin yawa, sa’an nan, a kan hanyarmu ta zuwa titin Shanghai, ko ina ana iya ganin gawawwakin fararen hula. A gabanmu, mun ga dakarun mamaya na kasar Japan.”

Cikin kundin, John Rabe ya rubuta ta’asar da sojojin Japan suka aikata a birnin Nanjing na kasar Sin, a ranar 13 ga watan Disamban shekarar ta 1937, hakan ya sa kundin ya kasance muhimmiyar shaida, da ta fayyace gaskiyar kisan kiyashin birnin Nanjing.

Dakarun mamaya na kasar Japan sun hallaka Sinawa 300,000, tare da cin zarafin mata masu dimbin yawa. Kazalika yara da yawa sun rasa rayukansu, kuma an rusa kaso 1 bisa 3 na daukacin gidajen birnin, tare da kwashe dukiyoyi masu dumbin yawa. Kisan kiyashin birnin Nanjing da dakarun mamaya na kasar Japan suka aikata, ya zama laifin cin zarafin dan Adam, kuma babu wanda zai iya musanta wannan lamari, ganin yadda aka tattara shaidu masu karfi dake tabbatar da aukuwarsa.

ADVERTISEMENT

To sai dai kuma ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar Japan ta ki amincewa da kuskuren da ta aikata na tayar da yaki, maimakon hakan ma, ana iya ganin masu aikata laifuffukan tayar da yakin suna dawowa teburin siyasar Japan, kana shugabanni, da manyan jami’an kasar da dama suna kai ziyara haikalin Yasukuni, inda suke girmama kaburburan mayakan da suka jagorancin aikata wancan ta’asa.

A farkon watan Nuwamban bana, firaministar kasar Japan Takaichi Sanae ta bayyana cewa, matsalar Taiwan tana da alaka da tsaron kasar Japan, inda ta nuna cewa, mai iyuwa ne kasar Japan ta dauki matakan soja, wajen tsoma hannu cikin harkokin Taiwan na kasar Sin. Wannan tsokacin da ta yi, ya yi kama da tsohuwar dabi’ar kasar Japan ta amfani da karfin soji.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Watsi da tarihi cin amana ne kana kin amincewa da aikata laifi tamkar sake aikawa ne. A bana, ake cika shekaru 80 da Sinawa suka samu nasara a yaki da maharan Japan da ma yakin duniya na II, kuma ba zai yiwu a musanta kisan kiyashin birnin Nanjing ba. Abubuwan da Takaichi Sanae, da ma sauran ‘yan siyasa da dama na kasar Japan suka aikata na musantawa da kokarin gyara tarihi, sun kasance laifi na farfado da dabi’ar Japan ta amfani da karfin soji, lamarin da ya illata dokar kasa da kasa, tare da gurgunta nasarar da aka cimma a yakin duniya na biyu, kana ya bakanta ran gamayyar kasa da kasa. Tabbas, tarihi zai wanzar da cewa, adalci, da haske, da kuma ci gaba, za su yi galaba kan yaki da rashin adalci, da duhu, da kuma tashe-tashen hankula! (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

Tarihi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Tarihi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Kafa Sabuwar Rundunar Tsaron Tashoshin Mota

Gwamnan Kano Ya Kafa Sabuwar Rundunar Tsaron Tashoshin Mota

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.