• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
in Siyasa
0
Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar zabe a jihar Katsina Alhaji Jibrin Ibrahim Zarewa, ya ba da tabbacin hada karfe da karfe da kungiyar darika awareness forum, wajan ci gaba da wayar da kan jama’a a kan abin da ya shafi hukumar zabe da kuma rijistar katin zabe da ake gudanarwa a fadin Nijeriya.

Zarewa ya bayyana haka a lokacin da shuwagabannin kungiyar suka kai masa ziyara a shalkwatar hukumar da ke Katsina.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa
  • ‘Yan Sanda Da ‘Yan Kasuwa Sun Yi Hadin Guiwa Don Kawo Karshen Kwacen Waya A Kano

Tunda farko dai shugaban ya yi wa tawagar kungiyar cikakken bayani game da ita kanta hukumar zabe da kuma irin ayyukan da doka ta sahale mata ta yi akan fannoni daban-daban.

Ya kuma nuna jin dadinsa da ziyarar  tare da fadin cewa INEC a shirye take ta yi aiki kafada da kafada da kungiyar, musamman a kan abinbda ya shafi wayar da kan jama’a kan batun katin zabe da sauran batutuwa a fadin jihar Katsina.

Haka kuma Zarewa, ya ce wannan ziyara an yi ta a lokacin da ya da ce, duk da cewa wuri ya kure amma dai kungiyar na da rawar da zata taka wajen ganin an kara samun narasa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Wani abu da ba ku sani ba shi ne, an yi wa jihar Katsina nisa wajen yin rijistar katin zabe, idan aka duba matsayin jihar Katsina ta hudu a yawan mutane da masu katin zaɓe, amma yanzu ta koma ta ashirin da hudu, wanda ba haka muka so ba” inji shi

Kazalika ya yi dogon bayani a kan yadda suka samu karin rumfunan zabe da wuraren da aka kai su, tare da daukar alkawarin cewa duk lokacin da hukumar za ta yi wani taro na masu ruwa da tsaki kungiyar na cikin sahun gaba saboda muhimmanci da irin tsare-tsaren da suke da shi.

Tunda da farko da yake nasa jawabin a kan makasudin wannan ziyara ta su, shugaban tafiyar kuma daya daga cikin kwamitin amintattu na kungiyar, Farfesa Abdulaziz Ahmad Mashi, ya bayyana cewa tuni suka so kawo ziyara amma yanzu Allah baya kaddara hakan.

Ya kara da cewa suna son hada gwuiwa da hukumar zabe domin ba da ta su gudunmawar wajen ganin jama’a sun yanki katin zabe kuma kungiyarsu ba ta da alaka ta nesa ko ta kusa da kowace irin jam’iyyar siyasa.

Farfesa Mashi, ya ce bisa haka ne suke neman cikakken bayani game da ayyukan wannan hukuma wanda hakan zai ba su damar sanin ta inda za su ba da gudunmawa ganin cewa mafi yawansu a tafiyar matasa ne.

Sannan ya nemi hukumar zabe da ta dauki kungiyar a matsayin abokiyar tafiya wajen isar da sako ga al’ummar Musulmi ba wai sai ‘yan darika kawai ba.

A nasa ta’alikin sakataren tsare -tsaren kungiyar, Awwal Abba Yahaya, ya ba da tarihin kafuwar kungiyar da kuma dalilin da ya sa aka kafa ta tare da yin bayanin irin tsarin shugabancin da suke da shi a matakin jiha da shiyya da kananan hukumomi zuwa mazabu.

Abba ya ce suna amfani da hanya mafi sauki wajen isar da kowane irin sako ake son isarwa ga mambobinsu, ko dai ta hanyar haduwa a Masallatai na yau da kullum ko kuma duk sati wajen zikirin Juma’a.

“Kimanin shekaru bakwai ke nan da kafa wannan kungiya wanda take da wakilin kowane bangare a darika kuma muna da shugabanni tun daga matakin jiha da shiyya da kuma kananan hukumomi, har da matakin rumfa, kuma babu ruwanmu da wata jam’iyyar siyasa, muna yin wanna tafiya ne ganin yadda aka bar mu a baya akan batun siyasa amma yanzu mun farka kuma za a damu da mu” inji shi

Daga karshe sakataran tsare-tsaren, ya ce sun shirya tsaf domin ci gaba da wayar da jama’a a kan wannan hidima ta katin zabe, inda ya ce za su yi amfani da kafafen yada labarai wajen isar da sakon, tare da ba da tabbacin za a ga canji nan kusa ba nesa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023Darika Awareness Forum KatsinaINECKada Kuri'aKatin ZabeSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

Next Post

Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

Related

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

2 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

3 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

4 days ago
Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani
Manyan Labarai

Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani

4 days ago
PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke
Siyasa

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

5 days ago
Next Post
Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.