• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

WTO Ta Yi Gargadin Fuskantar Matsin Tattalin Arziki A Duniya

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
WTO Ta Yi Gargadin Fuskantar Matsin Tattalin Arziki A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kasuwanci ta Duniya (WTO), ta yi gargadin cewa duniya na tunkarar wani yanayi na matsin tattalin arziki sakamakon rikice-rikice da dama, wanda ke nuna bukatar da ake da ita samar da sabbin tsare-tsare da za su habaka tattalin arziki.

Darakta-Janar ta WTO, Ngozi Okonjo-Iweala, ta bayyana cewa batutuwa masu alaka da yakin Rasha da Ukraine da kuma dumamar yanayi sun yi taron dangi wajen assasa tsadar kayayyaki musamman na abinci baya ga haddasa karancin makamashi a sassan duniya, dai-dai lokacin da ake shirin fita daga matsalar da annobar cutar Korona ta jefa duniya.

  • Buhari Ya Haramta Siyan Makamai Ga Jami’an Tsaron Sa-Kai A Jihohi
  • Amurka Ta Yi Kaurin Suna Wajen Kakaba Takunkumai

A jawabinta a wajen taron kasuwanci da zuba jari na shekara-shekara da ke gudana a Geneva, shugabar ta WTO ta ce wajibi ne a samar da sabbin dabarun habaka tattalin arziki da za su ragewa duniya radadin halin da ake ciki da kuma barazanar da ke tunkarowa.

A cewarta ana cikin wani yanayi da kiri-kiri ake iya hango barazanar da tattalin arziki ke tunkara wanda don haka dole a yi aiki tukuru wajen laluben hanyoyin murmurewa tun gabanin fadawa a matsalar baki daya, ta yadda za a dauki matakan rage tasirin da illar ta mashassharar tattalin arziki za ta yi wa Duniya.

Ngozi Okonjo-Iweala ta kafa hujja da yadda dukkanin hasashen tattalin arzikin da Bankin Duniya da kuma asusun bada lamuni na Duniya suka yi ke nuna mummunar koma bayan da ke tunkaro Duniya.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Darakta-Janar din, ta ce kasashe a yanzu na fama da matsalolin rashin tsaro, dumamar yanayi, tsadar kayan abinci da kuma tsadar makamashi wanda dukkaninsu a lokaci guda, wanda kai tsaye zai iya ruguza kasashe da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Darakta-JanarKoronaMatsin Tattalin ArzikiTsadar kayan abinciWTO
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mohammed Idris Malagi A Ma’aunin Siyasa

Next Post

Yadda Aka Yi Jana’izar Jarumin Kannywood, Umar Malumfashi

Related

Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

53 minutes ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

2 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

2 hours ago
Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

7 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

19 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

21 hours ago
Next Post
Yadda Aka Yi Jana’izar Jarumin Kannywood, Umar Malumfashi

Yadda Aka Yi Jana'izar Jarumin Kannywood, Umar Malumfashi

LABARAI MASU NASABA

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne ÆŠantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne ÆŠantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.