• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wunti Al-Khair Ta Horar Da ‘Yan Agaji Don Rage Cunkoso A Lokacin Sallar Idi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Wunti

Gidauniyar ‘Wunti Al-Khair Foundation’ ta horar da ‘yan agajin kungiyoyin Addini Musulunci don sanin dabarun yadda za su shawo kan cunkoso da saukaka zirga-zirga a lokacin bukukuwan karamar sallah a Jihar Bauchi.

Wani dan Jihar Bauchi da ya kasance mai gudanar da ayyukan taimakon al’umma da na jiin kai, Alhaji Bala Wunti, ne shugaban gidauniyar kuma shi ke daukan nauyin horo na tsawon kwanaki biyu da ya gudana a babban masallacin Fadar Sarki da ke Bauchi.

  • Al’adar Kallon Furannin Magnolia A Wurin Ibada Na Dajuesi Mai Tarihin Fiye Da Shekara Dubu
  • Sai A Hankali Zan Gyara Chelsea, Frank Lampard

Da ya ke jawabin bude horo, daraktan sashin agaji na Jama’atu Nasril Islam (JNI) Alhaji Bala Ibrahim Sani, ya ce, horon wanda Bala Wunti ya saba daukan nauyi na taimakawa sosai wa ‘yan agajin ta hanyar basu karin ilimin da ke taimaka musu wajen gudanar da ayyukansu.

Sani wanda shi ne Lifidin Bauchi ya ce, wannan horon shi ne karo na biyar da gidauniyar ke yi, ya misalta hakan a matsayin aikin aikairi sosai, “Iyaka abun da za mu ce wa Bala Wunti sai dai mu masa Allah ya saka masa da mafificiyar alkairi bisa irin gudunmawar da yake bayar wa addinin musulunci.”

Ya ce, a kalla ‘yan agaji 150 ne aka basu horon da za su je su ma su koyar da sauran abokan aikinsu ta yadda kwalliya za ta biya kudin sabulu.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

Ya kara da cewa an dauko jami’ai daga hukumar kiyaye aukuwar hadura (FRSC) da Red Cross da sauran hukumomin da abun ya shafa inda suke bai wa ‘yan agajin lakcoci da darussan da suka dace dukka domin tabbatar da an yi bikin sallah lafiya.

“Kuma muna da jami’an da suke yawan zuwa aikin hajji su na nazartar yadda ake shawo kan cinkoso da tabbatar da an kammala komai lafiya, don haka irin wannan horon na kara mana saninmu da gogewa a bangaren ayyukan hidimta wa jama’a da muke yi.”

A cewarsa a karshen bitan, gidauniyar na raba kyautar buhun shinkafa, shadda da zani ga kowani mahalaccin bitar.

Kwamandan ya yi amfani da wannan damar wajen rokon Bala Wunti da ya duba yiyuwar samar wa kungiyoyin agaji da motocin daukan marasa lafiya a cibiyoyin addinin musulunci da Masallatai.

Ya ce, “Duk shekara idan wasu ‘yan agaji sun zo a wata shekara sai a canza a kawo wasu, hikimar haka shi ne kowa zai samu ilimin da ake nema.”

A cewarsa kowace shekara ana horar da ‘yan agajin ne kan yadda za su kiyaye cinkoson ababen hawa tare da saukaka wa jama’a yadda za su yi zirga-zirga a lokacin bukukuwan sallah. Sai ya ce a bana sun kara gayyato jami’ai daga hukumar kashe gobara domin basu horon kan kashe gobara musamman a lokacin da ake bukatar agajin gaggawa.

A nasa jawabin wani malamin addinin musulunci a jihar Bauchi, Sheikh Bala Isa ya nuna matukar farin cikinsa a bisa yadda Bala Wunti ke gudanar da ayyukan taimakon al’umma da suka kunshi Gina masallatai, cibiyar da mabukata, tallafa wa marasa karfi da dai sauransu.

Ya ce, horon ya zama wani karin hadin kai a tsakanin kungiyoyin agaji, ya ce taimakon da wannan horon bayarwa ba karamin fa’ida yake da shi ba. Ya bayyana cewar wannan horaswar zai taimaka gaya domin kuwa ‘yan agajin su na buqatar karin sani kan hidimar inganta aikinsu domin samun dabararrun aiki.

A nasa jawabin, Alhaji Bala Wunti, ya ce, yana shirya horaswar ne da nufin taimakawa wajen ganin an gudanar da sallar Idi lafiya ba tare da wani matsala ba.

Bala Wunti wanda shi ne babban manajan rukunin ‘National Petroleum Investment Management Services’ (NAPIMS), wanda ya samu wakilcin Kabiru Garba Aminu, ya nuna kwarin guiwarsa na cewa da irin wannan hadin kan da ake samu tsakanin kungiyoyin agaji za a kara samun kyakkyawar fahimta. Ya nemi masu samun horon da su maida hankali su ribanci abun da ake koya musu.

Alhaji Bala Wunti ya shaida cewar manufar shirya taron sh ine domin a samar wa ‘yan agajin ilimin sanin makamar aiki kamar yadda ya dace, yana mai shaida cewar mafiya yawan qungiyoyin agaji na addini basu da cikakken ilimin yadda za su bayar da agajin gaggawa ko kuma magance wani matsalar masu kawo cikas a lokacin da suke bakin aikinsu, sai ya bayyana cewar hakan ne ya sanya shirya taron domin a samar da ci gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

katsina
Labarai

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Abduljabbar
Labarai

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Next Post
Da Dumi-dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 30, Sun Banka Wa Gidaje Wuta A Kudancin Kaduna

Da Dumi-dumi: 'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 30, Sun Banka Wa Gidaje Wuta A Kudancin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.