• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wunti Al-Khair Ta Horar Da ‘Yan Agaji Don Rage Cunkoso A Lokacin Sallar Idi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Wunti Al-Khair Ta Horar Da ‘Yan Agaji Don Rage Cunkoso A Lokacin Sallar Idi A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gidauniyar ‘Wunti Al-Khair Foundation’ ta horar da ‘yan agajin kungiyoyin Addini Musulunci don sanin dabarun yadda za su shawo kan cunkoso da saukaka zirga-zirga a lokacin bukukuwan karamar sallah a Jihar Bauchi.

Wani dan Jihar Bauchi da ya kasance mai gudanar da ayyukan taimakon al’umma da na jiin kai, Alhaji Bala Wunti, ne shugaban gidauniyar kuma shi ke daukan nauyin horo na tsawon kwanaki biyu da ya gudana a babban masallacin Fadar Sarki da ke Bauchi.

  • Al’adar Kallon Furannin Magnolia A Wurin Ibada Na Dajuesi Mai Tarihin Fiye Da Shekara Dubu
  • Sai A Hankali Zan Gyara Chelsea, Frank Lampard

Da ya ke jawabin bude horo, daraktan sashin agaji na Jama’atu Nasril Islam (JNI) Alhaji Bala Ibrahim Sani, ya ce, horon wanda Bala Wunti ya saba daukan nauyi na taimakawa sosai wa ‘yan agajin ta hanyar basu karin ilimin da ke taimaka musu wajen gudanar da ayyukansu.

Sani wanda shi ne Lifidin Bauchi ya ce, wannan horon shi ne karo na biyar da gidauniyar ke yi, ya misalta hakan a matsayin aikin aikairi sosai, “Iyaka abun da za mu ce wa Bala Wunti sai dai mu masa Allah ya saka masa da mafificiyar alkairi bisa irin gudunmawar da yake bayar wa addinin musulunci.”

Ya ce, a kalla ‘yan agaji 150 ne aka basu horon da za su je su ma su koyar da sauran abokan aikinsu ta yadda kwalliya za ta biya kudin sabulu.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Ya kara da cewa an dauko jami’ai daga hukumar kiyaye aukuwar hadura (FRSC) da Red Cross da sauran hukumomin da abun ya shafa inda suke bai wa ‘yan agajin lakcoci da darussan da suka dace dukka domin tabbatar da an yi bikin sallah lafiya.

“Kuma muna da jami’an da suke yawan zuwa aikin hajji su na nazartar yadda ake shawo kan cinkoso da tabbatar da an kammala komai lafiya, don haka irin wannan horon na kara mana saninmu da gogewa a bangaren ayyukan hidimta wa jama’a da muke yi.”

A cewarsa a karshen bitan, gidauniyar na raba kyautar buhun shinkafa, shadda da zani ga kowani mahalaccin bitar.

Kwamandan ya yi amfani da wannan damar wajen rokon Bala Wunti da ya duba yiyuwar samar wa kungiyoyin agaji da motocin daukan marasa lafiya a cibiyoyin addinin musulunci da Masallatai.

Ya ce, “Duk shekara idan wasu ‘yan agaji sun zo a wata shekara sai a canza a kawo wasu, hikimar haka shi ne kowa zai samu ilimin da ake nema.”

A cewarsa kowace shekara ana horar da ‘yan agajin ne kan yadda za su kiyaye cinkoson ababen hawa tare da saukaka wa jama’a yadda za su yi zirga-zirga a lokacin bukukuwan sallah. Sai ya ce a bana sun kara gayyato jami’ai daga hukumar kashe gobara domin basu horon kan kashe gobara musamman a lokacin da ake bukatar agajin gaggawa.

A nasa jawabin wani malamin addinin musulunci a jihar Bauchi, Sheikh Bala Isa ya nuna matukar farin cikinsa a bisa yadda Bala Wunti ke gudanar da ayyukan taimakon al’umma da suka kunshi Gina masallatai, cibiyar da mabukata, tallafa wa marasa karfi da dai sauransu.

Ya ce, horon ya zama wani karin hadin kai a tsakanin kungiyoyin agaji, ya ce taimakon da wannan horon bayarwa ba karamin fa’ida yake da shi ba. Ya bayyana cewar wannan horaswar zai taimaka gaya domin kuwa ‘yan agajin su na buqatar karin sani kan hidimar inganta aikinsu domin samun dabararrun aiki.

A nasa jawabin, Alhaji Bala Wunti, ya ce, yana shirya horaswar ne da nufin taimakawa wajen ganin an gudanar da sallar Idi lafiya ba tare da wani matsala ba.

Bala Wunti wanda shi ne babban manajan rukunin ‘National Petroleum Investment Management Services’ (NAPIMS), wanda ya samu wakilcin Kabiru Garba Aminu, ya nuna kwarin guiwarsa na cewa da irin wannan hadin kan da ake samu tsakanin kungiyoyin agaji za a kara samun kyakkyawar fahimta. Ya nemi masu samun horon da su maida hankali su ribanci abun da ake koya musu.

Alhaji Bala Wunti ya shaida cewar manufar shirya taron sh ine domin a samar wa ‘yan agajin ilimin sanin makamar aiki kamar yadda ya dace, yana mai shaida cewar mafiya yawan qungiyoyin agaji na addini basu da cikakken ilimin yadda za su bayar da agajin gaggawa ko kuma magance wani matsalar masu kawo cikas a lokacin da suke bakin aikinsu, sai ya bayyana cewar hakan ne ya sanya shirya taron domin a samar da ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GidauniyaKungiyaSallar Idi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’adar Kallon Furannin Magnolia A Wurin Ibada Na Dajuesi Mai Tarihin Fiye Da Shekara Dubu

Next Post

Da Dumi-dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 30, Sun Banka Wa Gidaje Wuta A Kudancin Kaduna

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

4 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

5 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

6 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

7 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

7 hours ago
Next Post
Da Dumi-dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 30, Sun Banka Wa Gidaje Wuta A Kudancin Kaduna

Da Dumi-dumi: 'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 30, Sun Banka Wa Gidaje Wuta A Kudancin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.