ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wunti Al-Khair Ta Horar Da ‘Yan Agaji Don Rage Cunkoso A Lokacin Sallar Idi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Wunti

Gidauniyar ‘Wunti Al-Khair Foundation’ ta horar da ‘yan agajin kungiyoyin Addini Musulunci don sanin dabarun yadda za su shawo kan cunkoso da saukaka zirga-zirga a lokacin bukukuwan karamar sallah a Jihar Bauchi.

Wani dan Jihar Bauchi da ya kasance mai gudanar da ayyukan taimakon al’umma da na jiin kai, Alhaji Bala Wunti, ne shugaban gidauniyar kuma shi ke daukan nauyin horo na tsawon kwanaki biyu da ya gudana a babban masallacin Fadar Sarki da ke Bauchi.

  • Al’adar Kallon Furannin Magnolia A Wurin Ibada Na Dajuesi Mai Tarihin Fiye Da Shekara Dubu
  • Sai A Hankali Zan Gyara Chelsea, Frank Lampard

Da ya ke jawabin bude horo, daraktan sashin agaji na Jama’atu Nasril Islam (JNI) Alhaji Bala Ibrahim Sani, ya ce, horon wanda Bala Wunti ya saba daukan nauyi na taimakawa sosai wa ‘yan agajin ta hanyar basu karin ilimin da ke taimaka musu wajen gudanar da ayyukansu.

ADVERTISEMENT

Sani wanda shi ne Lifidin Bauchi ya ce, wannan horon shi ne karo na biyar da gidauniyar ke yi, ya misalta hakan a matsayin aikin aikairi sosai, “Iyaka abun da za mu ce wa Bala Wunti sai dai mu masa Allah ya saka masa da mafificiyar alkairi bisa irin gudunmawar da yake bayar wa addinin musulunci.”

Ya ce, a kalla ‘yan agaji 150 ne aka basu horon da za su je su ma su koyar da sauran abokan aikinsu ta yadda kwalliya za ta biya kudin sabulu.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Ya kara da cewa an dauko jami’ai daga hukumar kiyaye aukuwar hadura (FRSC) da Red Cross da sauran hukumomin da abun ya shafa inda suke bai wa ‘yan agajin lakcoci da darussan da suka dace dukka domin tabbatar da an yi bikin sallah lafiya.

“Kuma muna da jami’an da suke yawan zuwa aikin hajji su na nazartar yadda ake shawo kan cinkoso da tabbatar da an kammala komai lafiya, don haka irin wannan horon na kara mana saninmu da gogewa a bangaren ayyukan hidimta wa jama’a da muke yi.”

A cewarsa a karshen bitan, gidauniyar na raba kyautar buhun shinkafa, shadda da zani ga kowani mahalaccin bitar.

Kwamandan ya yi amfani da wannan damar wajen rokon Bala Wunti da ya duba yiyuwar samar wa kungiyoyin agaji da motocin daukan marasa lafiya a cibiyoyin addinin musulunci da Masallatai.

Ya ce, “Duk shekara idan wasu ‘yan agaji sun zo a wata shekara sai a canza a kawo wasu, hikimar haka shi ne kowa zai samu ilimin da ake nema.”

A cewarsa kowace shekara ana horar da ‘yan agajin ne kan yadda za su kiyaye cinkoson ababen hawa tare da saukaka wa jama’a yadda za su yi zirga-zirga a lokacin bukukuwan sallah. Sai ya ce a bana sun kara gayyato jami’ai daga hukumar kashe gobara domin basu horon kan kashe gobara musamman a lokacin da ake bukatar agajin gaggawa.

A nasa jawabin wani malamin addinin musulunci a jihar Bauchi, Sheikh Bala Isa ya nuna matukar farin cikinsa a bisa yadda Bala Wunti ke gudanar da ayyukan taimakon al’umma da suka kunshi Gina masallatai, cibiyar da mabukata, tallafa wa marasa karfi da dai sauransu.

Ya ce, horon ya zama wani karin hadin kai a tsakanin kungiyoyin agaji, ya ce taimakon da wannan horon bayarwa ba karamin fa’ida yake da shi ba. Ya bayyana cewar wannan horaswar zai taimaka gaya domin kuwa ‘yan agajin su na buqatar karin sani kan hidimar inganta aikinsu domin samun dabararrun aiki.

A nasa jawabin, Alhaji Bala Wunti, ya ce, yana shirya horaswar ne da nufin taimakawa wajen ganin an gudanar da sallar Idi lafiya ba tare da wani matsala ba.

Bala Wunti wanda shi ne babban manajan rukunin ‘National Petroleum Investment Management Services’ (NAPIMS), wanda ya samu wakilcin Kabiru Garba Aminu, ya nuna kwarin guiwarsa na cewa da irin wannan hadin kan da ake samu tsakanin kungiyoyin agaji za a kara samun kyakkyawar fahimta. Ya nemi masu samun horon da su maida hankali su ribanci abun da ake koya musu.

Alhaji Bala Wunti ya shaida cewar manufar shirya taron sh ine domin a samar wa ‘yan agajin ilimin sanin makamar aiki kamar yadda ya dace, yana mai shaida cewar mafiya yawan qungiyoyin agaji na addini basu da cikakken ilimin yadda za su bayar da agajin gaggawa ko kuma magance wani matsalar masu kawo cikas a lokacin da suke bakin aikinsu, sai ya bayyana cewar hakan ne ya sanya shirya taron domin a samar da ci gaba.

Wunti
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Da Dumi-dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 30, Sun Banka Wa Gidaje Wuta A Kudancin Kaduna

Da Dumi-dumi: 'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 30, Sun Banka Wa Gidaje Wuta A Kudancin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.