ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sai A Hankali Zan Gyara Chelsea, Frank Lampard

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Lampard

Sabon mai koyar da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Frank Lampard ya ce baya jin za’a magance matsalar Chelsea a rana daya, bayan da ya fara da kafar hagu a Wolberhampton.

Lampard wanda ya ja ragamar Chelsea a karon farko a matakin rikon kwarya, ya yi rashin nasara 1-0 a gidan Wolbes a wasan mako na 30 a Premier ranar Asabar a filin wasa na Moulined.

  • Wang Yi Da Qin Gang Sun Gana Da Ministar Harkokin Wajen Jamus 
  • Kin Amincewa Da Kwangilar Dala Miliyan 22 Ta Yi Sanadiyyar Sauke Ni Daga Shugabancin NPA –Hajiya Hadiza Bala-Usman

Wasan farko da ya shugabancin Chelsea tun bayan watanni 27 da aka kore shi a Stamford Bridge, Thomas Tuchel ya maye gurbinsa wanda shi ma daga baya aka kore shi.

ADVERTISEMENT

Chelsea ta kasa zura kwallo a raga a wasanni uku a jere kenan, karo na 11 da aka doke ta a babbar gasar firimiyar Ingila ta kakar nan wanda hakan ba karamin ci baya bane ga kungiyar.

”Mun kwana da sani ba ma yanayi mai kyau, ba wanda muke bukata bane, amma da akwai dalilin hakan ban jin zan warware matsalar nan a kwana daya, dole sai mun kara kwazo a wasa da sa kaimi.” In ji Lampard.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Wasa hudu kenan da Chelsea ba ta yi nasara ba, wadda a ranar Laraba ta je gidan Real Madrid, domin buga Champions League kuma a sati mai zuwa kungiyoyin za su sake karawa a filin wasa na Stamford Bridge.

Lampard, wanda bai da kungiya tun bayan da Eberton ta sallame shi a watan Janairun 2023, ya horar da Chelsea daga watan Yulin 2019 zuwa Janairun 2021 daga nan ta kore shi.

An nada shi kociyan rikon kwarya zuwa karshen kakar nan a makon nan, bayan da Chelsea ta kori Graham Potter a karshen watan daya gabata, wanda ya yi watanni bakwai kacal yana koyar da kungiyar.

Tun farko Chelsea ta sa Potter ya yi murabus daga aikin Brighton, sannan ta kulla yarjejeniyar shekara biyar da shi saboda rashin tabuka abin arziki ya sa kungiyar ta sallame shi.

Lampard ya buga wa Chelsea wasa a Stamford Bridge lokacin da Roberto di Matteo ya ja ragamar kungiyar ta lashe Champions League a 2012 a matakin rikon kwarya daga baya aka bashi jan ragama.

Lampard
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
PDP Ta Bukaci A Kama Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

PDP Ta Bukaci A Kama Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.