Babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, ya jaddada bukatar kara aiwatar da dabarun kara karfin sojojin kasar, ta hanyar horar da kwararrun sojoji a sabon zamani.
Yayin da yake jagoranta tare da gabatar da jawabi a taron nazari na rukunin ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS da ya gudana jiya Alhamis, Xi Jinping ya kuma bukaci da a yi kokarin ba da gudummawar da ta dace ga rawar da masu hazaka ke takawa wajen jagoranci da tabbatar da gina rundunar soja mai karfi.(Ibrahim)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp