• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaƙi Da ‘Yan Bindiga: Yadda Gwamna Dauda Ya Karɓi Baƙuncin Babban Hafsan Tsaro

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Yaƙi Da ‘Yan Bindiga: Yadda Gwamna Dauda Ya Karɓi Baƙuncin Babban Hafsan Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya tabbatar wa rundunar sojojin ƙasar nan jajircewar gwamnatinsa wajen bai wa jami’an soji cikakken goyon bayan gwamnatin sa a jihar Zamfara. 

 

Ranar Juma’ar da ta gabata, Gwamna Lawal ya karɓi baƙuncin Babban Hafsan tsaron ƙasa (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa a tsohon ɗakin taron fadar gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 40 A Hatsarin Kwale-kwale
  • Bukukuwan Mauludi: Wani Mummunan Hatsari Ya Ci Rayukan Mutane 40 A Saminaka

Sanarwa daga mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ta bayyana cewa Babban Hafsan tsaron ya sanar da wani laƙabi da za a rinƙa kiran rundunar haɗin gwiwa ta yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Yamma, inda ya ce za a rinƙa kiranta da ‘rundunar samamen Fansan Yamma, wanda kuma yanzu ita ce rundunar da aka sani a yankin Arewa maso Yamma.

 

Labarai Masu Nasaba

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

Sanarwar ta ci gaba da cewa, wannan runduna ta ‘Operation Fansan Yamma,’ wani laƙabi ne da ke nuni da cewa jami’an tsaron a shirye su ke don ganin sun murƙushe harkar ‘yan bindiga a yankin na Arewa maso Yamma.

 

Cikin jawabin sa, Gwamna Dauda ya yaba wa Babban Hafsan bisa irin namijin ƙoƙarin da ya ke yi wajen magance matsalolin tsaro a ƙasar nan.

Bindiga

“Janar, kasancewarka a Zamfara a wannan lokaci, ya ƙara ƙara wa jami’an soji ƙwarin gwiwa. Ka ƙara tabbatar da fatan mu, al’umma na cike da fata.

 

“Ba za mu taɓa yin wasa da wannan ziyara ba. Gwamnatina ta jajirce wajen haɗa kai da Hukumomin tsaro don tabbatar da tsaro a jihar Zamfara.

 

“Bisa la’akari da jawabinka, ina da tabbacin cewa zaman lafiya zai dawo a Zamfara. Ka yi makaranta a nan, ka san irin yanayin zaman lafiyar da ake da shi a da. Gusau ta kasance birni na biyu a harkar Kasuwanci a Arewa bayan jihar Kano.

 

“Na ji daɗin kasacewa kana aiki tare da rundunar Askarawan Zamfara ta CPG. Ina so ka sani, kafin a zaɓi Askarawan Zamfara sai da Hukumar tsaro ta DSS da sauran hukumomin tsaro suka tantance su.

 

“Muna bayar da cikakken goyon bayan mu ga sojoji a ƙoƙarin su na yaƙi da ‘yan bindiga. An tura waɗannan jami’ai zuwa yankunan su. Muna da yaƙinin cewa sojoji a jajirce suke wajen magance matsalar tsaro.

 

“Zan yi amfani da wannan dama wajen miƙa ta’aziyyata bisa jajirtattun jami’an da suka rasu a hanyar Gusau zuwa Funtuwa. Allah gafarta masu. Ina tabbatar maka da cewa gwamnatina na tare da kai, kuma za mu ci gaba da aiki tare da jami’an soji da sauran hukumomin tsaro don kawo ƙarshen ‘yan bindiga.”

Bindiga

Tun farko a jawabinsa, Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Gwabin Musa, ya nuna matuƙar godiyar sa ga Gwamna Dauda Lawal bisa goyon bayan da ya ke bai wa sojoji da sauran jami’an tsaro a jihar. “Mun zo nan ne don muna godiyar mu bisa irin goyon bayan da ka ke bai wa sojoji da sauran jami’an tsaro, tare da irin gagarumar ci gaban da kake samarwa a jihar Zamfara.

 

“Na kasance ina alfahari da Gusau da na sani, amma gaskiya, yanzu abin da na gani, sai na rasa me zan ce. Yabon gwani ya zama dole bisa irin ci gaban da ka samar wa Zamfara a shekara ɗaya kacal, a ƙarƙashin jagorancinka. Ina gode maka bisa inganta rayuwar al’umma. Wannan romon Dimokraɗiyya ne. Muna ganin ci gaba da dama, tare da wasu ayyukan da ake gudanarwa a jihar, tun bayan hawan ka mulki.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BaleriYaki da Yan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Next Post

WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

Related

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura
Manyan Labarai

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

10 hours ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

11 hours ago
Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari

11 hours ago
Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura
Manyan Labarai

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

12 hours ago
Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina
Manyan Labarai

Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina

13 hours ago
HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura
Hotuna

HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura

15 hours ago
Next Post
WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.