• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata CBN Ya Saurari Koke-koken Al’umma – Alhaji Ibrahim

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
CBN

Gamayyar kungiyoyin matasan arewa mazauna Legas sun bayyana cewa lallai Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya saurari koke-koken al’ummar kasar nan wajen kara yawan adadin kudaden da za a dunga cirewa a duk kullum.

A baya dai, CBN ya kakaba dokar kayyade cire kudade wanda a duk kulum mutum zai iya cire naira 20,000, yayin da a mako mutum zai iya cire naira 100,000 kacal.

  • Kotu Ta Sake Hana DSS Cafke Gwamnan CBN, Godwin Emefiele
  • NIS Ta Bankado Sabbin Dabarun Da Masu Safarar Mutane Ke Amfani Da Su A Jihar Bayelsa

Sai dai daga baya CBN ya kara yawan kudaden ya tashi daga naira 100,000 zuwa naira 500,000 a duk mako. Inda kamfanoni za su iya cire naira miliyan 5 maimakon dubu dari biyar a mako. Dokar kayyade kudaden za ta fara aiki ne tun daga ranar 9 ga watan Janairun 2023.

Mafi yawancin al’ummar Nijeriya sun nuna gamsuwarsu game da wannan mataki da CBN ya dauka na kara yawan kudaden, wanda suke ganin cewa lallai CBN ya saurari koke-koken al’ummar kasar nan.

Shugaban gamayyar, Alhaji Ibrahim Galadanci ne ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labarai.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Ya ce, “A matsayina na wadanda muke mu’amala da al’umma muna ganin sauya wannan salo da CBN ya sauya ya ji kiran talakawa. Ma’ana gwamnati ta sausauta wa marasa karfi.

“Dama mu abin da muke hange a nan shi ne, salon da CBN ya dauka kan wannan dokar kayyade kudade, ya faru ne sakamakon bata-garin ‘yan siyasa da suke wadaka da kudaden al’umma. An kakaba wannan doka ne saboda a taimaka wa al’umma, domin akwai wadanda suke sana’a a bangaren harkokin kudi da suka yi rajista da POS.

“Kamar mutumin karkara wanda ba lallai ba ne sai ya je banki. Zai iya sayar da amfanin gonarsa ya samu mai POS ya ba shi ‘yar dubu darinsa ya saka masa a asusun bankinsa.

“Tsarin da gwamnati ta bullo da shi a wannan karan, mu dai a bangarenmu gwamnati ba ta taba yin wani abu wanda muka ji dadinsa sama da wannan ba. Domin gwamnati ta fito da doka kuma ‘yan kasa suka fito suka yi ta korafi a kan gwamnati ta sassauta kuma har ta saurari koke-koken al’umma,” in ji Ibrahim Galadanci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Bikin Nadin Sabon Sarkin Jere Na 11 Ya Kayatar

Bikin Nadin Sabon Sarkin Jere Na 11 Ya Kayatar

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.