• Leadership Hausa
Thursday, September 21, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Nadin Sabon Sarkin Jere Na 11 Ya Kayatar

by Abdulrazaq Yahuza
9 months ago
in Masarautu
0
Bikin Nadin Sabon Sarkin Jere Na 11 Ya Kayatar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Juma’a ne Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmed El-Rufa’i ya rantsar da mai martaba sabon Sarkin Jere na 11, Alhaji Abdullahi Daniya a wani gagarumin bikin da aka gudanar a babban filin kwallon kafa na garin Jere.

Bikin wanda ya gudana cikin tsattsauran tsaro, ya samu halartar mataimakiyar gwamnan, Hajiya Hadiza Balarabe da kusan daukacin ‘yan majalisar zartaswa na Jihar Kaduna, da mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli, da Jakadan Nijeriya a Kasar Benin, Janar Yusuf Tukur Buratai mai ritaya da Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, Isah Jere Idris da sauran manyan baki daga ko ina a sassan kasar nan.

  • Zan Fi Mayar Da Hankali Kan Ilimi Da Matasa – Kwankwaso
  • NIS Ta Bankado Sabbin Dabarun Da Masu Safarar Mutane Ke Amfani Da Su A Jihar Bayelsa

Da yake jawabi bayan rantsarwar, Gwamna El-Rufai ya jaddada muhimmancin zaman lafiya a tsakanin al’umma wanda ya ce shi ne babban ginshikin kawo ci gaba mai ma’ana. Ya yaba wa al’ummar Jere bisa yadda suka rungumi zaman lafiya tare da yin jaje ga wadanda barnar ‘yan bindiga ta shafa.

Ya kara da cewa, gwamnati na ci gaba da yin duk abin da za ta iya wajen tabbatar da tsaro a fadin Jihar Kaduna, kana ya nemi a kara bai wa jami’an tsaro hadin kai domin su ji dadin dorewa da kwazon da suke nunawa a yanzu haka wajen fatattakar ‘yan ta’addar.

Wakazalika, Gwamna El-Rufai ya yi tsokaci a kan matakan da gwamnatinsa take ci gaba da daukawa wajen kare martabar sarakuna da daga darajojinsu a Jihar Kaduna, inda ya yi nuna da cewa an raba wa Hakimai motoci kuma a yanzu haka gwamnatin na shirin sake raba wasu motoci 88 duk dai ga sarakuna a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Bikin Bai Wa Sarkin Kagara Sandar Girma Ya Gudana

Dakta Olusola Saraki: Shekara 10 Da Rasuwar Dattijon Arziki, Baya Goya Marayu

Ya yi kira ga al’ummar Jere su martaba sabon sarkin nasu da ba shi hadin kai don ya ji dadin sauke nauyin da aka dora masa na jama’a. Daga nan ya yi addu’ar Allah ya gafarta wa Sarkin Jere na 10, Dakta Sa’ad Usman.

Shi ma da yake jawabi, Shugaban Karamar Hukumar Kagarko, Honarabul Auzara Rabo, ya gode wa Gwamna El-Rufai bisa bisa gagarumin ci gaban da ya kawo yankin karamar hukumar da bai wa matasa dama a dama da su a fagen siyasa wanda ya ce hakan ne ya sa aka samu matashi a karon farko da ke shugabantar karamar hukumar.

A nasa jawabin, mai martaba Sarkin Jere, Alhaji Abdullahi Daniya, ya gode wa dukkan jama’ar da suka halarci bikin, sannan ya jaddada kudirinsa na kara hada kan al’umma da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin masarautar.

Daga bisani, Sarkin Jere ya nada Gwamna El-Rufai sarautar Sarkin Yakin Jere tare da mika masa malafa, da sandar kiwo da kuma katon bajimin sa domin kiwo.

Tags: JereKadunaSarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata CBN Ya Saurari Koke-koken Al’umma – Alhaji Ibrahim

Next Post

Gobara Ta Lalata Gidaje, Mutane Sun Bace A Ribas

Related

Jere
Masarautu

Yadda Bikin Bai Wa Sarkin Kagara Sandar Girma Ya Gudana

10 months ago
Dakta Olusola Saraki: Shekara 10 Da Rasuwar Dattijon Arziki, Baya Goya Marayu
Manyan Labarai

Dakta Olusola Saraki: Shekara 10 Da Rasuwar Dattijon Arziki, Baya Goya Marayu

10 months ago
Gwamnan Bauchi Ya Mika Wa Sarkin Katagum Sandar Girma
Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Mika Wa Sarkin Katagum Sandar Girma

10 months ago
Bagudu Ya Amince Da Nadin Sarakunan Gargajiya 2 A Masarautar Yauri Ta Jihar Kebbi
Masarautu

Bagudu Ya Amince Da Nadin Sarakunan Gargajiya 2 A Masarautar Yauri Ta Jihar Kebbi

10 months ago
Zabarmawa Sun Yi Gagarumin Taro A Kebbi
Masarautu

Zabarmawa Sun Yi Gagarumin Taro A Kebbi

1 year ago
Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa
Masarautu

Dakta Bashir Bala Getso Ya Zama Jakadan Hausawa

1 year ago
Next Post
Gobara Ta Lalata Gidaje, Mutane Sun Bace A Ribas

Gobara Ta Lalata Gidaje, Mutane Sun Bace A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

September 21, 2023
Yawan Jarin Da Sin Ta Zuba A Ketare Daga Janairu Zuwa Agusta Ya Rika Karuwa

Yawan Jarin Da Sin Ta Zuba A Ketare Daga Janairu Zuwa Agusta Ya Rika Karuwa

September 21, 2023
Super Eagles Ta Nijeriya Ta Dawo Mataki Na 40 A Jadawalin Kasashen Da Suka Fi Iya Taka Leda A Duniya

Super Eagles Ta Nijeriya Ta Dawo Mataki Na 40 A Jadawalin Kasashen Da Suka Fi Iya Taka Leda A Duniya

September 21, 2023
Sin Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kare Mabanbantan Halittun Teku

Sin Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kare Mabanbantan Halittun Teku

September 21, 2023
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Zhejiang

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Zhejiang

September 21, 2023
Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

September 21, 2023
IPC

IPC Ta Yi Tir Da Muzguna Wa ‘Yan Jarida Yayin Daukan Rahoton Shari’ar Kujerar Gwamna A Kano

September 21, 2023
Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

September 21, 2023
An Dawo Da Biyan Tallafin Man Fetur: Gwamnatin Tarayya Ta Biya Naira Biliyan 169.4 A Watan Agusta

An Dawo Da Biyan Tallafin Man Fetur: Gwamnatin Tarayya Ta Biya Naira Biliyan 169.4 A Watan Agusta

September 21, 2023
NUJ Ta Yi Kira Ga Jami’an Tsaro Da Su Gaggauta Zakulo Wadanda Suka Yi Wa Danjarida Kisan Gilla A Zamfara

NUJ Ta Yi Kira Ga Jami’an Tsaro Da Su Gaggauta Zakulo Wadanda Suka Yi Wa Danjarida Kisan Gilla A Zamfara

September 21, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.