• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Nadin Sabon Sarkin Jere Na 11 Ya Kayatar

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Masarautu
0
Bikin Nadin Sabon Sarkin Jere Na 11 Ya Kayatar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Juma’a ne Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmed El-Rufa’i ya rantsar da mai martaba sabon Sarkin Jere na 11, Alhaji Abdullahi Daniya a wani gagarumin bikin da aka gudanar a babban filin kwallon kafa na garin Jere.

Bikin wanda ya gudana cikin tsattsauran tsaro, ya samu halartar mataimakiyar gwamnan, Hajiya Hadiza Balarabe da kusan daukacin ‘yan majalisar zartaswa na Jihar Kaduna, da mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli, da Jakadan Nijeriya a Kasar Benin, Janar Yusuf Tukur Buratai mai ritaya da Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, Isah Jere Idris da sauran manyan baki daga ko ina a sassan kasar nan.

  • Zan Fi Mayar Da Hankali Kan Ilimi Da Matasa – Kwankwaso
  • NIS Ta Bankado Sabbin Dabarun Da Masu Safarar Mutane Ke Amfani Da Su A Jihar Bayelsa

Da yake jawabi bayan rantsarwar, Gwamna El-Rufai ya jaddada muhimmancin zaman lafiya a tsakanin al’umma wanda ya ce shi ne babban ginshikin kawo ci gaba mai ma’ana. Ya yaba wa al’ummar Jere bisa yadda suka rungumi zaman lafiya tare da yin jaje ga wadanda barnar ‘yan bindiga ta shafa.

Ya kara da cewa, gwamnati na ci gaba da yin duk abin da za ta iya wajen tabbatar da tsaro a fadin Jihar Kaduna, kana ya nemi a kara bai wa jami’an tsaro hadin kai domin su ji dadin dorewa da kwazon da suke nunawa a yanzu haka wajen fatattakar ‘yan ta’addar.

Wakazalika, Gwamna El-Rufai ya yi tsokaci a kan matakan da gwamnatinsa take ci gaba da daukawa wajen kare martabar sarakuna da daga darajojinsu a Jihar Kaduna, inda ya yi nuna da cewa an raba wa Hakimai motoci kuma a yanzu haka gwamnatin na shirin sake raba wasu motoci 88 duk dai ga sarakuna a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

Ya yi kira ga al’ummar Jere su martaba sabon sarkin nasu da ba shi hadin kai don ya ji dadin sauke nauyin da aka dora masa na jama’a. Daga nan ya yi addu’ar Allah ya gafarta wa Sarkin Jere na 10, Dakta Sa’ad Usman.

Shi ma da yake jawabi, Shugaban Karamar Hukumar Kagarko, Honarabul Auzara Rabo, ya gode wa Gwamna El-Rufai bisa bisa gagarumin ci gaban da ya kawo yankin karamar hukumar da bai wa matasa dama a dama da su a fagen siyasa wanda ya ce hakan ne ya sa aka samu matashi a karon farko da ke shugabantar karamar hukumar.

A nasa jawabin, mai martaba Sarkin Jere, Alhaji Abdullahi Daniya, ya gode wa dukkan jama’ar da suka halarci bikin, sannan ya jaddada kudirinsa na kara hada kan al’umma da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin masarautar.

Daga bisani, Sarkin Jere ya nada Gwamna El-Rufai sarautar Sarkin Yakin Jere tare da mika masa malafa, da sandar kiwo da kuma katon bajimin sa domin kiwo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JereKadunaSarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata CBN Ya Saurari Koke-koken Al’umma – Alhaji Ibrahim

Next Post

Gobara Ta Lalata Gidaje, Mutane Sun Bace A Ribas

Related

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)
Masarautu

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

6 months ago
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)
Masarautu

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

11 months ago
Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa
Labarai

Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa

11 months ago
Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)
Masarautu

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

12 months ago
Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla
Masarautu

Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla

12 months ago
Tinubu Zai Halarci  Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa
Addini

Tinubu Zai Halarci Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa

12 months ago
Next Post
Gobara Ta Lalata Gidaje, Mutane Sun Bace A Ribas

Gobara Ta Lalata Gidaje, Mutane Sun Bace A Ribas

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.