• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ƙungiyar Matasan Arewa Kan Harkokin Tsaro Ta Shirya Tattaunawa Kan Batun ‘Yansandan Jihohi

by Sani Anwar
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Yadda Ƙungiyar Matasan Arewa Kan Harkokin Tsaro Ta Shirya Tattaunawa Kan Batun ‘Yansandan Jihohi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Matasan Nijeriya Kan Harkokin Tsaro (CONYSSA), ta shirya taron masu ruwa da tsaki na ƙasa; domin tattaunawa a kan shawawarin da ake yi game da samar da ‘yansandan jiha a faɗin jihohi 36 na tarayya wanda aka gudanar a Cibiyar Bunƙasa Al’amuran Sojoji da ke Abuja (Army Resource Centre).

Da yake yin nasa wajibin a wajen taron da aka shirya tare da haɗin gwiwar Rundunar ‘Yansandan Nijeriya, Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Dakta Isa Yuguda ya yi tsokaci kan cewa, wajibi ne a zurfafa bincike a kan ƙalubalen da ke fuskantar jami’an ‘yansanda da sauran jami’an tsaron wannan ƙasa, matuƙar ana so su ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukansu.

Yuguda ya ƙara da cewa, a matsayin Nijeriya ta ƙasa; dole ne ta ƙara ƙaimi wajen sanin matsalolin da ke addabar waɗannan jami’ai, kafin ta kai ga cimma nasarar da take buƙata a tsakaninsu.

Ya ƙara jaddada cewa, “ƙasar da take da ingantaccen tsaro, ita ce wadda zuba jari ke matuƙar bunƙasa a cikinta. Don haka, kafin Nijeriya ta kai ga matsayin da ake buƙata a fannin tsaro, dole ne ta sake jajircewa tare da samun mutane masu matuƙar kishi, ɗa’a, ƙwarewa, aikin yi da kuma adalci a tsakanin al’umma.

Tsaro
Har ila yau, tsohon gwamnan; ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga sauran al’ummar ƙasa, domin su farka tare da kasancewa cikin shiri; don sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na tallafa wa gwamnati tsakaninsu da Allah, domin ganin an samu ci gaban ƙasa.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Kazalika, ya buƙaci mahalarta wannan taro da a koda-yaushe su riƙa tunanin samar da mafita tare da ci gaban ƙasar baki-ɗaya.
Ya ci gaba da cewa, “Muna buƙatar gyara ‘yansandanmu, domin abin tambaya shi ne; shin sun samu horo mai kyau, suna samun albashi mai kyau, suna da ingantattatun kayan aiki, suna samun horon da ya kamata ɗansanda ya samu ko kuma a’a kawai abin da ake cewa; muna ɗansanda ne?
Saboda haka, “Wajibi ne mu fara magance matsalolin da suka shafi ‘yansanda, maimakon ƙirƙirar wasu ‘yansandan waɗanda za su iya zama haɗari ko barazana da makamai a hannunsu.”

Haka zalika, shi ma a nasa tsokacin; Mai Martaba Cif Ayini Clement, wanda yake da ra’ayin samar da waɗannan ‘yansanda na jihohi ya bayyana cewa, akwai buƙatar a ƙara wa ‘yansandan tarayya ƙwarin gwiwa, domin samun damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Tsaro
Cif ya ƙara da cewa, fa’idar samar da ‘yansandan jihohi ita ce, duk yankin da aka ɗauki ɗansanda aiki; ya san lungu da saƙo na wannan waje tare da dukkanin al’ummar da ke zaune a yankin.

Haka zalika, shi ma Darakta Janar mai kula da harkokin tsaro da binciken shari’a a Nijeriya, Dakta Okocha Morgan; ya yi kira ga gwamnati da ta taka muhimmiyar rawa wajen kawo sauyi tare da sake fasalin harkokin tsaro a Nijeriya, wanda ya haɗa da horar da ma’aikata da kuma ɗaukar wasu ƙwararrun ma’aikatan.

Bugu da ƙari, tun da farko; Darakta Janar na wannan ƙungiya ta Haɗin Kan Matasan Nijeriya Kan Harkokin Tsaro (CONYSA), Ambasada Ade Emmanuel ya ce, manufar wannan taro shi ne; tattaunawa a kan muhimmanci ko rashin muhimmancin samar da ‘yansandan jihohi da ake ta faman taƙaddama a kansa.

“Babu shakka, matasa na da gudunmawar da za su iya bayarwa; domin yaƙi da rashin tsaro matuƙar an yi amfani da su yadda ya dace, sannan ‘yansandan jihohi na iya samun ci gaba a wasu ƙasashen da suka ci gaba; suke da kuma kishin ƙasa fiye da mu, amma aiwatar da shi a nan ko shakka babu; na iya haifar da mummunan rikici.

Saboda haka, “ya kamata gwamnatocin jihohi su yi aiki yadda ya kamata da ‘yansandan tarayya, domin samun sauƙi, inganci da kuma ɗorewar zaman lafiya a faɗin wannan ƙasa baki-ɗaya.

Har ila yau, taron ya samu halartar wakilan hukumomin soja da na jami’an tsaro daban-daban a Nijeriya da kuma sauran masu ruwa da tsaki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaƘungiyaTaroTattaunawaTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Sayi Motoci Masu Amfani Da Gas

Next Post

2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

2 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

2 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

3 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

3 weeks ago
Next Post
2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

LABARAI MASU NASABA

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.