• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ƙungiyar Matasan Arewa Kan Harkokin Tsaro Ta Shirya Tattaunawa Kan Batun ‘Yansandan Jihohi

by Sani Anwar
12 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Yadda Ƙungiyar Matasan Arewa Kan Harkokin Tsaro Ta Shirya Tattaunawa Kan Batun ‘Yansandan Jihohi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Matasan Nijeriya Kan Harkokin Tsaro (CONYSSA), ta shirya taron masu ruwa da tsaki na ƙasa; domin tattaunawa a kan shawawarin da ake yi game da samar da ‘yansandan jiha a faɗin jihohi 36 na tarayya wanda aka gudanar a Cibiyar Bunƙasa Al’amuran Sojoji da ke Abuja (Army Resource Centre).

Da yake yin nasa wajibin a wajen taron da aka shirya tare da haɗin gwiwar Rundunar ‘Yansandan Nijeriya, Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Dakta Isa Yuguda ya yi tsokaci kan cewa, wajibi ne a zurfafa bincike a kan ƙalubalen da ke fuskantar jami’an ‘yansanda da sauran jami’an tsaron wannan ƙasa, matuƙar ana so su ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukansu.

Yuguda ya ƙara da cewa, a matsayin Nijeriya ta ƙasa; dole ne ta ƙara ƙaimi wajen sanin matsalolin da ke addabar waɗannan jami’ai, kafin ta kai ga cimma nasarar da take buƙata a tsakaninsu.

Ya ƙara jaddada cewa, “ƙasar da take da ingantaccen tsaro, ita ce wadda zuba jari ke matuƙar bunƙasa a cikinta. Don haka, kafin Nijeriya ta kai ga matsayin da ake buƙata a fannin tsaro, dole ne ta sake jajircewa tare da samun mutane masu matuƙar kishi, ɗa’a, ƙwarewa, aikin yi da kuma adalci a tsakanin al’umma.

Tsaro
Har ila yau, tsohon gwamnan; ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga sauran al’ummar ƙasa, domin su farka tare da kasancewa cikin shiri; don sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na tallafa wa gwamnati tsakaninsu da Allah, domin ganin an samu ci gaban ƙasa.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Kazalika, ya buƙaci mahalarta wannan taro da a koda-yaushe su riƙa tunanin samar da mafita tare da ci gaban ƙasar baki-ɗaya.
Ya ci gaba da cewa, “Muna buƙatar gyara ‘yansandanmu, domin abin tambaya shi ne; shin sun samu horo mai kyau, suna samun albashi mai kyau, suna da ingantattatun kayan aiki, suna samun horon da ya kamata ɗansanda ya samu ko kuma a’a kawai abin da ake cewa; muna ɗansanda ne?
Saboda haka, “Wajibi ne mu fara magance matsalolin da suka shafi ‘yansanda, maimakon ƙirƙirar wasu ‘yansandan waɗanda za su iya zama haɗari ko barazana da makamai a hannunsu.”

Haka zalika, shi ma a nasa tsokacin; Mai Martaba Cif Ayini Clement, wanda yake da ra’ayin samar da waɗannan ‘yansanda na jihohi ya bayyana cewa, akwai buƙatar a ƙara wa ‘yansandan tarayya ƙwarin gwiwa, domin samun damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Tsaro
Cif ya ƙara da cewa, fa’idar samar da ‘yansandan jihohi ita ce, duk yankin da aka ɗauki ɗansanda aiki; ya san lungu da saƙo na wannan waje tare da dukkanin al’ummar da ke zaune a yankin.

Haka zalika, shi ma Darakta Janar mai kula da harkokin tsaro da binciken shari’a a Nijeriya, Dakta Okocha Morgan; ya yi kira ga gwamnati da ta taka muhimmiyar rawa wajen kawo sauyi tare da sake fasalin harkokin tsaro a Nijeriya, wanda ya haɗa da horar da ma’aikata da kuma ɗaukar wasu ƙwararrun ma’aikatan.

Bugu da ƙari, tun da farko; Darakta Janar na wannan ƙungiya ta Haɗin Kan Matasan Nijeriya Kan Harkokin Tsaro (CONYSA), Ambasada Ade Emmanuel ya ce, manufar wannan taro shi ne; tattaunawa a kan muhimmanci ko rashin muhimmancin samar da ‘yansandan jihohi da ake ta faman taƙaddama a kansa.

“Babu shakka, matasa na da gudunmawar da za su iya bayarwa; domin yaƙi da rashin tsaro matuƙar an yi amfani da su yadda ya dace, sannan ‘yansandan jihohi na iya samun ci gaba a wasu ƙasashen da suka ci gaba; suke da kuma kishin ƙasa fiye da mu, amma aiwatar da shi a nan ko shakka babu; na iya haifar da mummunan rikici.

Saboda haka, “ya kamata gwamnatocin jihohi su yi aiki yadda ya kamata da ‘yansandan tarayya, domin samun sauƙi, inganci da kuma ɗorewar zaman lafiya a faɗin wannan ƙasa baki-ɗaya.

Har ila yau, taron ya samu halartar wakilan hukumomin soja da na jami’an tsaro daban-daban a Nijeriya da kuma sauran masu ruwa da tsaki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaƘungiyaTaroTattaunawaTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Sayi Motoci Masu Amfani Da Gas

Next Post

2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

1 month ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.